< Ru’uya ta Yohanna 14 >

1 Sai na duba, can a gabana kuwa ga Ɗan Rago, tsaye a kan Dutsen Sihiyona, tare da shi akwai kuma mutane 144,000 waɗanda suke da sunansa da sunan Ubansa a rubuce a goshinsu.
I looked, and saw the Lamb standing on Mount Zion. With him were 144,000 who had his name, and the name of his Father, written on their foreheads.
2 Sai na ji ƙara daga sama kamar motsin ruwaye masu gudu, kamar kuma tsawa. Ƙarar da na ji ta yi kamar ta masu garaya da suke kiɗin garayarsu.
I heard a voice from heaven that sounded like rushing water and loud thunder and many harps being played.
3 Suka kuwa rera sabuwar waƙa a gaban kursiyin da kuma a gaban halittu huɗun nan masu rai, da kuma a gaban dattawa. Ba wanda ya iya koyon waƙar sai mutanen nan 144,000 da aka fansa daga duniya.
They sang a new song in front of the throne and the four living creatures and the elders. Nobody could learn the song except the 144,000, those who had been redeemed from the earth.
4 Waɗannan su ne waɗanda ba su ƙazantar da kansu da mata ba, gama sun kiyaye kansu da tsarki. Suna bin Ɗan Ragon duk inda ya tafi. Su ne aka saya daga cikin mutane aka kuwa miƙa su kamar’ya’yan fari ga Allah da kuma Ɗan Ragon.
They have not become morally impure by sinning with women; spiritually they are virgins. They follow the Lamb wherever he goes. They were redeemed from humankind as the firstfruits to God and the Lamb.
5 Ba a sami ƙarya a bakunansu ba; su kuma marasa aibi ne.
They speak no lies; they are without fault.
6 Sai na ga wani mala’ika yana tashi sama a tsakiyar sararin sama, yana kuma da madawwamiyar bishara wadda zai yi shela ga waɗanda suke zama a duniya, ga kowace al’umma, kabila, harshe, da kuma jama’a. (aiōnios g166)
Then I saw another angel flying in mid-heaven. He had the eternal good news to announce to those who lived on the earth, to every nation, tribe, language, and people. (aiōnios g166)
7 Ya ce da babbar murya, “Ku ji tsoron Allah ku kuma ɗaukaka shi, domin sa’ar hukuncinsa ya yi. Ku yi wa wannan da ya halicci sammai, ƙasa, teku, da maɓulɓulan ruwa sujada.”
He cried out in a loud voice, “Give God reverence and glory, for the time of his judgment has come. Worship the one who made heaven and earth and sea and springs of water.”
8 Mala’ika na biyu ya biyo yana cewa, “Ta fāɗi! Babilon Mai Girma ta fāɗi, wadda ta sa dukan al’ummai suka sha ruwan inabin hauka na zinanta.”
A second angel followed, calling out, “Babylon the great has collapsed into ruins! She made all the nations drink the wine of her sexual immorality that brings God's furious opposition.”
9 Mala’ika na uku ya biyo su ya ce da babbar murya, “Duk wanda ya yi wa dabban nan da siffarta sujada ya kuma sami alamarta a goshi ko a hannu,
A third angel followed the first two, and cried out in a loud voice, “If anyone worships the beast and his image and receives a mark on their forehead or on their hand,
10 shi ma zai sha ruwan inabin fushin Allah, wanda aka zuba da duk ƙarfinsa a kwaf fushinsa. Za a ba shi azaba da farar wuta mai ci a gaban tsarkakan mala’iku da na Ɗan Ragon.
they will also drink of the wine of God's furious opposition that is poured undiluted into the cup of his anger, and they will suffer anguish in fire and burning sulfur before the holy angels and the Lamb.
11 Hayaƙin azabarsu kuwa zai dinga tashi har abada abadin. Kuma babu hutu dare ko rana wa waɗanda suke wa dabbar da siffarta sujada, ko kuwa ga duk wanda ya sami alamar sunanta.” (aiōn g165)
The smoke of their anguish ascends for ever and ever. They don't have any relief day or night, those who worship the beast and his image and who receive the mark of his name.” (aiōn g165)
12 Wannan yana bukata haƙuri, a gefen tsarkakan da suke biyayya da umarnan Allah suka kuma kasance da aminci ga Yesu.
This means the believers must patiently endure, keeping God's commandments and trusting in Jesus.
13 Sai na ji murya daga sama ta ce, “Rubuta, Masu albarka ne matattun da suka mutu cikin Ubangiji daga yanzu zuwa gaba.” “I, za su huta daga faman aikinsu, gama ayyukansu za su bi su,” in ji Ruhu.
Then I heard a voice from heaven that told me, “Write this down! Blessed are the dead who die in the Lord from now on. Yes, says the Spirit, because they can rest from their troubles. What they have accomplished will speak for them.”
14 Na duba, can gabana kuwa ga farin girgije, zaune kuma a kan girgijen kuwa ga wani da ya yi kamar “ɗan mutum” tare da rawanin zinariya a kansa da kuma lauje mai kaifi a hannunsa.
I looked and I saw a white cloud. Sitting on the cloud was someone that looked like the Son of man, wearing a golden crown on his head and holding a sharp sickle in his hand.
15 Sai wani mala’ika ya fito daga haikali ya kuma yi kira da babbar murya ga wannan mai zaune a kan girgijen ya ce, “Ɗauki laujenka ka yi girbi, domin lokacin girbi ya yi, gama amfanin da yake duniya ya nuna.”
Another angel came out of the Temple and shouted in a loud voice to the one sitting on the cloud, “Take your sickle and start reaping, for it is harvest-time, and earth's harvest is ripe.”
16 Sai wannan mai zaune a girgijen ya wurga laujensa a duniya, sai aka kuwa girbe duniya.
The one sitting on the cloud swung his sickle towards the earth, and reaped earth's harvest.
17 Wani mala’ika kuma ya fito daga haikali a sama, shi ma yana da lauje mai kaifi.
Another angel came out of the Temple in heaven. He also had a sharp sickle.
18 Har yanzu, wani mala’ika mai lura da wuta, ya fito daga bagaden ya yi kira da babbar murya ga wannan wanda yake da lauje mai kaifi ya ce, “Ɗauki laujenka mai kaifi ka tattara kawunan’ya’yan inabi daga kuringar inabin duniya, domin’ya’yan inabin sun nuna.”
He was followed by an angel coming from the altar that was in charge of the fire, who called in a loud voice to the angel with the sharp sickle, “Take your sharp sickle and harvest the bunches of grapes from the earth's vine, because its grapes are ripe.”
19 Mala’ikan ya wurga laujensa a duniya, ya tattara’ya’yan inabin, ya kuma zuba su cikin babbar wurin matsewar inabin fushin Allah.
The angel swung his sickle on the earth and harvested the grapes from the vine, and threw them into the great winepress of God's judgment.
20 Aka tattake su a wurin matsin inabi a bayan gari, jini kuwa ya yi ta gudana daga wurin matsin inabi tsayinsa ya kai kamar tsawon linzami a bakin doki, nisansa kuma ya kai wajen kilomita 300.
They were trampled in the winepress outside the city. Blood flowed out of the winepress to the height of a horse's bridle, and to a distance of 1,600 stadia.

< Ru’uya ta Yohanna 14 >