< Ru’uya ta Yohanna 13 >
1 Macijin kuwa ya tsaya a bakin teku. Sai na ga wata dabba tana fitowa daga teku. Tana da ƙahoni goma da kawuna bakwai, da kuma rawani goma a ƙahoninta, a kowane kai kuwa akwai sunan saɓo.
E o dragão ficou em pé na praia. E, então, vi um monstro que surgia do mar. Ele tinha dez chifres e sete cabeças, com dez pequenas coroas em seus chifres e tinha nomes que eram blasfêmias, escritos em suas cabeças.
2 Dabbar da na gani ta yi kamar damisa, amma tana da ƙafafu kamar na beyar, bakinta kuma ya yi kamar na zaki. Macijin nan ya ba wa dabbar ƙarfinsa da gadon sarautarsa da kuma ikonsa mai girma.
O monstro que eu vi se parecia com um leopardo, mas os seus pés pareciam patas de um urso e a sua boca era como a de um leão. O dragão deu para o monstro o seu poder, o seu trono e grande autoridade.
3 Ɗaya daga cikin kawunan dabbar ya yi kamar yana da raunin da zai iya kashe shi, amma raunin nan da zai iya kashe shi ya riga ya warke. Dukan duniya ta yi mamaki ta kuma bi dabbar.
Uma das suas cabeças parecia ter sido golpeada mortalmente, mas essa ferida fatal tinha sido curada. O mundo todo ficou maravilhado com o dragão
4 Mutane suka yi wa macijin sujada domin ya ba wa dabbar ikonsa, suka yi wa dabbar sujada, suka kuma yi tambaya cewa, “Wane ne yake kama da dabban nan? Wa zai iya yaƙe ta?”
e começaram a adorá-lo, porque ele tinha dado a sua autoridade para o monstro. E as pessoas também adoravam o monstro, perguntando: “Quem tem tanto poder quanto o monstro? Quem poderia vencê-lo?”
5 Aka ba wa dabbar baki don ta faɗi kalmomin girman kai da na saɓo ta kuma yi amfani da ikonta har watanni arba’in da biyu.
Ele recebeu a habilidade de contar grandes vantagens e de dizer blasfêmias, além de receber também a autoridade para fazer isso durante quarenta e dois meses.
6 Ta buɗe bakinta don tă yi wa Allah saɓo, ta kuma ɓata sunansa da kuma mazauninsa da na waɗanda suke zama a sama.
Assim que abriu a sua boca, falou blasfêmias contra Deus, insultando o caráter do Senhor, o seu santuário e aqueles que vivem no céu.
7 Aka ba ta iko tă yaƙi tsarkaka tă kuma ci nasara a kansu. Aka kuma ba ta iko bisa kowace kabila, jama’a, harshe da kuma al’umma.
O monstro recebeu o poder de atacar o povo de Deus e de derrotá-lo. Ele também ganhou do dragão a autoridade sobre todos os povos, tribos, línguas e nações.
8 Dukan mazaunan duniya za su yi wa dabbar sujada, dukan waɗanda ba a rubuta sunayensu a cikin littafin ran da yake na Ɗan Ragon da aka yanka tun kafin halittar duniya ba.
Todos que moram no mundo irão adorá-lo, todos os que não têm os seus nomes escritos no Livro da Vida, desde a fundação do mundo. Esse livro pertence ao Cordeiro, que foi morto.
9 Duk mai kunne ji, bari yă ji.
Se vocês têm ouvidos, ouçam!
10 Duk wanda aka ƙaddara ga bauta, ga bauta zai tafi. Duk wanda aka ƙaddara za a kashe da takobi, da takobin za a kashe shi. Wannan yana bukata haƙuri da aminci a gefen tsarkaka.
Quem tiver que ser preso, será preso; quem tiver que morrer pela espada, morrerá pela espada. Isso demonstra a perseverança paciente e a confiança em Deus dos irmãos na fé.
11 Sai na ga wata dabba tana fitowa daga ƙasa. Tana da ƙahoni biyu kamar ɗan rago, amma ta yi magana kamar maciji.
Então, eu vi outro monstro, surgindo da terra. Ele tinha dois chifres como um carneiro, mas falava como um dragão.
12 Ta mori dukan ikon dabban nan ta fari a madadinta, ta sa duniya da mazaunanta su yi wa dabba ta farin nan sujada, wadda aka warkar mata da raunin nan da zai iya kashe ta.
Ele exerce a mesma autoridade que o primeiro monstro, na sua presença, e faz com que a terra e aqueles que nela vivem adorem o primeiro monstro, de quem a ferida fatal tinha sido curada.
13 Ta kuma yi manyan ayyuka da kuma alamu masu banmamaki, har ta sa wuta ta sauko daga sama zuwa ƙasa a gaban idon mutane.
Ele realizou grandes milagres, trazendo até mesmo fogo do céu para a terra, enquanto as pessoas olhavam admiradas.
14 Saboda alamun nan da aka ba ta iko tă yi a madadin dabban nan ta fari, sai ta ruɗi mazaunan duniya. Ta umarce su su kafa siffa don girmama dabbar da aka ji mata rauni da takobi duk da haka ta rayu.
Enganou aqueles que vivem na terra, por meio dos milagres que realizava em nome do monstro. Ordenou que as pessoas fizessem uma imagem para o monstro, que tinha um ferimento fatal feito por espada, mas que voltou à vida.
15 Aka ba ta iko tă ba da numfashi ga siffar dabban nan ta fari, don tă yi magana tă kuma sa a kashe duk waɗanda suka ƙi yi wa siffar sujada.
Ele recebeu permissão para soprar vida na imagem do primeiro monstro, para que ela pudesse falar e ordenar que quem não a adorasse fosse condenado à morte.
16 Ta kuma tilasta wa kowa, manya da yara, mawadata da matalauta,’yantattu da bayi, don a yi musu alama a hannun dama ko a goshi,
Ele fez com que todos, importantes e humildes, ricos ou pobres, livres ou escravos, recebessem um sinal na mão direita ou na testa.
17 don kada kowa yă saya ko yă sayar, sai dai yana da alamar, wadda take sunan dabbar ko kuma lambar sunanta.
Ninguém poderia comprar ou vender, a não ser que tivesse o sinal. Esse sinal era o nome do monstro, ou o número do seu nome.
18 Wannan yana bukata hikima. Duk mai hankali, sai yă lissafta lambar dabbar, gama lamban nan ta mutum ne. Lambarta kuwa ita ce 666.
É preciso ter sabedoria aqui. Quem tiver entendimento pode descobrir o número do monstro, pois é o número de um homem. O seu número é 666.