< Ru’uya ta Yohanna 13 >

1 Macijin kuwa ya tsaya a bakin teku. Sai na ga wata dabba tana fitowa daga teku. Tana da ƙahoni goma da kawuna bakwai, da kuma rawani goma a ƙahoninta, a kowane kai kuwa akwai sunan saɓo.
And I stood upon the sand of the sea, and saw a savage beast ascending out of the sea, having seven heads and ten horns; and upon its horns were ten diadems; and on its heads were the named of defamation.
2 Dabbar da na gani ta yi kamar damisa, amma tana da ƙafafu kamar na beyar, bakinta kuma ya yi kamar na zaki. Macijin nan ya ba wa dabbar ƙarfinsa da gadon sarautarsa da kuma ikonsa mai girma.
And the beast which I saw was like a leopard, and its feet were like those of a bear, and its mouth like the mouth of a lion; and the dragon gave it his power, and his throne, and great authority.
3 Ɗaya daga cikin kawunan dabbar ya yi kamar yana da raunin da zai iya kashe shi, amma raunin nan da zai iya kashe shi ya riga ya warke. Dukan duniya ta yi mamaki ta kuma bi dabbar.
And I saw one of its heads wounded, as it were, to death; and yet its mortal wound was healed. And the whole earth wondered, and followed after the wild beast;
4 Mutane suka yi wa macijin sujada domin ya ba wa dabbar ikonsa, suka yi wa dabbar sujada, suka kuma yi tambaya cewa, “Wane ne yake kama da dabban nan? Wa zai iya yaƙe ta?”
and they worshiped the dragon who gave authority to the wild beast, saying, Who is like to the beast? who can war against it?
5 Aka ba wa dabbar baki don ta faɗi kalmomin girman kai da na saɓo ta kuma yi amfani da ikonta har watanni arba’in da biyu.
And there was given to it a mouth speaking great things, and defamation: and there was given to it power to practice forty-two months--
6 Ta buɗe bakinta don tă yi wa Allah saɓo, ta kuma ɓata sunansa da kuma mazauninsa da na waɗanda suke zama a sama.
and it opened its mouth to utter defamation against God; to defame his name and his tabernacle, and those that dwell in heaven.
7 Aka ba ta iko tă yaƙi tsarkaka tă kuma ci nasara a kansu. Aka kuma ba ta iko bisa kowace kabila, jama’a, harshe da kuma al’umma.
And it was given to it to make war with the saints, and to overcome them: and there was given to it power over every tribe, and tongue, and nation.
8 Dukan mazaunan duniya za su yi wa dabbar sujada, dukan waɗanda ba a rubuta sunayensu a cikin littafin ran da yake na Ɗan Ragon da aka yanka tun kafin halittar duniya ba.
And all the inhabitants of the earth shall worship it, whose names are not written in the book of life of the Lamb, that was slain from the beginning of the world.
9 Duk mai kunne ji, bari yă ji.
If any one has an ear, let him hear.
10 Duk wanda aka ƙaddara ga bauta, ga bauta zai tafi. Duk wanda aka ƙaddara za a kashe da takobi, da takobin za a kashe shi. Wannan yana bukata haƙuri da aminci a gefen tsarkaka.
If any one lead them into captivity, he shall be led into captivity: if any one slay with the sword, he shall himself be slain with the sword. Here is the patience and the faith of the saints.
11 Sai na ga wata dabba tana fitowa daga ƙasa. Tana da ƙahoni biyu kamar ɗan rago, amma ta yi magana kamar maciji.
And I saw another beast ascending out of the earth, and it had two horns like a lamb: but it spoke like a dragon.
12 Ta mori dukan ikon dabban nan ta fari a madadinta, ta sa duniya da mazaunanta su yi wa dabba ta farin nan sujada, wadda aka warkar mata da raunin nan da zai iya kashe ta.
And it exercises all the power of the first beast, in its presence; and it makes the earth, and those that dwell in it, to worship the first beast, whose deadly wound was healed.
13 Ta kuma yi manyan ayyuka da kuma alamu masu banmamaki, har ta sa wuta ta sauko daga sama zuwa ƙasa a gaban idon mutane.
And it does great miracles, so as to make fire come down from heaven to earth, before men;
14 Saboda alamun nan da aka ba ta iko tă yi a madadin dabban nan ta fari, sai ta ruɗi mazaunan duniya. Ta umarce su su kafa siffa don girmama dabbar da aka ji mata rauni da takobi duk da haka ta rayu.
and it deceives the inhabitants of the earth by signs which it is given it to do before the beast; commanding the inhabitants of the earth to make an image of the beast that had the wound of the sword, and lived.
15 Aka ba ta iko tă ba da numfashi ga siffar dabban nan ta fari, don tă yi magana tă kuma sa a kashe duk waɗanda suka ƙi yi wa siffar sujada.
And it was given to it to give breath to the image of the beast, that the image of the beast might speak, and cause as many as will not worship the image of the beast to be put to death.
16 Ta kuma tilasta wa kowa, manya da yara, mawadata da matalauta,’yantattu da bayi, don a yi musu alama a hannun dama ko a goshi,
And he causes all, both small and great, rich and poor, freemen and slaves, to receive the mark on their right hand, or on their foreheads;
17 don kada kowa yă saya ko yă sayar, sai dai yana da alamar, wadda take sunan dabbar ko kuma lambar sunanta.
and that no one should be able to buy or sell, but one who has the mark, the name of the beast, or the number of its name.
18 Wannan yana bukata hikima. Duk mai hankali, sai yă lissafta lambar dabbar, gama lamban nan ta mutum ne. Lambarta kuwa ita ce 666.
Here is wisdom: let him who has understanding, compute the number of the beast; for it is the number of a man; and its number is six hundred and sixty-six.

< Ru’uya ta Yohanna 13 >