< Ru’uya ta Yohanna 13 >

1 Macijin kuwa ya tsaya a bakin teku. Sai na ga wata dabba tana fitowa daga teku. Tana da ƙahoni goma da kawuna bakwai, da kuma rawani goma a ƙahoninta, a kowane kai kuwa akwai sunan saɓo.
And I stood on the sand of the sea, and saw a beast coming up out of the sea, and he had seven heads and ten horns, and on his horns ten diadems, and on his heads names impiously irreverent.
2 Dabbar da na gani ta yi kamar damisa, amma tana da ƙafafu kamar na beyar, bakinta kuma ya yi kamar na zaki. Macijin nan ya ba wa dabbar ƙarfinsa da gadon sarautarsa da kuma ikonsa mai girma.
And the beast that I saw was like a leopard, and his feet were as those of a bear, and his mouth was as the mouth of a lion. And the dragon gave him his power, and his throne, and great authority.
3 Ɗaya daga cikin kawunan dabbar ya yi kamar yana da raunin da zai iya kashe shi, amma raunin nan da zai iya kashe shi ya riga ya warke. Dukan duniya ta yi mamaki ta kuma bi dabbar.
And I saw one of his heads as if it had been wounded even to death; and his deadly wound was healed; and all the earth wondered after the beast.
4 Mutane suka yi wa macijin sujada domin ya ba wa dabbar ikonsa, suka yi wa dabbar sujada, suka kuma yi tambaya cewa, “Wane ne yake kama da dabban nan? Wa zai iya yaƙe ta?”
And they worshiped the dragon, because he gave authority to the beast: and they worshiped the beast, saying, Who is like the beast? and, Who is able to make war with him?
5 Aka ba wa dabbar baki don ta faɗi kalmomin girman kai da na saɓo ta kuma yi amfani da ikonta har watanni arba’in da biyu.
And there was given him a mouth that spoke great things and impious words; and authority was given to him to continue forty-two months.
6 Ta buɗe bakinta don tă yi wa Allah saɓo, ta kuma ɓata sunansa da kuma mazauninsa da na waɗanda suke zama a sama.
And he opened his mouth in impious speeches against God, to utter impious words against his name, and his tabernacle, and against those who dwell in heaven.
7 Aka ba ta iko tă yaƙi tsarkaka tă kuma ci nasara a kansu. Aka kuma ba ta iko bisa kowace kabila, jama’a, harshe da kuma al’umma.
And it was given him to make war with the saints, and to overcome them: and authority was given him over every tribe and people and tongue and nation.
8 Dukan mazaunan duniya za su yi wa dabbar sujada, dukan waɗanda ba a rubuta sunayensu a cikin littafin ran da yake na Ɗan Ragon da aka yanka tun kafin halittar duniya ba.
And all that dwell upon the earth will worship him, those whose names are not written in the book of life of the Lamb that was slain from the foundation of the world.
9 Duk mai kunne ji, bari yă ji.
If any one has an ear, let him hear.
10 Duk wanda aka ƙaddara ga bauta, ga bauta zai tafi. Duk wanda aka ƙaddara za a kashe da takobi, da takobin za a kashe shi. Wannan yana bukata haƙuri da aminci a gefen tsarkaka.
If any one leads into captivity, he shall go into captivity. If any kills with the sword, he must be killed with the sword. Here is the patience and faithfulness of the saints.
11 Sai na ga wata dabba tana fitowa daga ƙasa. Tana da ƙahoni biyu kamar ɗan rago, amma ta yi magana kamar maciji.
And I saw another beast coming up out of the earth; and he had two horns like a lamb, and he spoke as a dragon.
12 Ta mori dukan ikon dabban nan ta fari a madadinta, ta sa duniya da mazaunanta su yi wa dabba ta farin nan sujada, wadda aka warkar mata da raunin nan da zai iya kashe ta.
And he exercises all the authority of the first beast in his presence; and he causes the earth and those who dwell in it to worship the first beast, whose deadly wound was healed.
13 Ta kuma yi manyan ayyuka da kuma alamu masu banmamaki, har ta sa wuta ta sauko daga sama zuwa ƙasa a gaban idon mutane.
And he does great signs, and even causes fire to descend from heaven upon the earth in the sight of men.
14 Saboda alamun nan da aka ba ta iko tă yi a madadin dabban nan ta fari, sai ta ruɗi mazaunan duniya. Ta umarce su su kafa siffa don girmama dabbar da aka ji mata rauni da takobi duk da haka ta rayu.
And he deceives those who dwell on the earth, by means of the signs which he is allowed to do in the presence of the beast, saying to those who dwell on the earth, that they should make an image for the beast which had the wound by the sword, and did live.
15 Aka ba ta iko tă ba da numfashi ga siffar dabban nan ta fari, don tă yi magana tă kuma sa a kashe duk waɗanda suka ƙi yi wa siffar sujada.
And it was granted him to give spirit to the image of the beast, that the image of the beast should both speak, and cause as many as would not worship the image of the beast, to be killed.
16 Ta kuma tilasta wa kowa, manya da yara, mawadata da matalauta,’yantattu da bayi, don a yi musu alama a hannun dama ko a goshi,
And he causes all, small and great, rich and poor, free and bond, to receive a mark on their right hand, or on their forehead,
17 don kada kowa yă saya ko yă sayar, sai dai yana da alamar, wadda take sunan dabbar ko kuma lambar sunanta.
and that no one should be able to buy or sell, but he that had the mark, the name of the beast, or the number of his name.
18 Wannan yana bukata hikima. Duk mai hankali, sai yă lissafta lambar dabbar, gama lamban nan ta mutum ne. Lambarta kuwa ita ce 666.
Here is wisdom. Let him that has understanding, count the number of the beast: for it is the number of a man, and his number is six hundred and sixty-six.

< Ru’uya ta Yohanna 13 >