< Ru’uya ta Yohanna 12 >

1 Babbar alama mai banmamaki ta bayyana a sama, mace tana lulluɓe da rana, da kuma wata a ƙarƙashin sawunta, akwai kuma rawani mai taurari goma sha biyu a kanta.
And a greet signe apperide in heuene; a womman clothid with the sunne, and the moone vndur hir feet, and in the heed of hir a coroun of twelue sterris.
2 Tana da ciki ta kuma yi kuka mai zafi yayinda take gab da haihuwa.
And sche hadde in wombe, and sche crieth, trauelynge of child, and is turmentid, that sche bere child.
3 Sai wata alama ta bayyana a sama, wani babban jan maciji mai kawuna bakwai da ƙahoni goma da rawani bakwai a kan kawunansa.
And another signe was seyn in heuene; and lo! a greet reede dragoun, that hadde seuene heedis, and ten hornes, and in the heedis of hym seuene diademes.
4 Wutsiyarsa ta share kashi ɗaya bisa uku na taurari daga sararin sama ta kuma zubar da su ƙasa. Ƙaton jan macijin ya tsaya a gaban macen wadda take gab da haihuwa, don yă cinye ɗanta nan take bayan an haife shi.
And the tail of hym drow the thridde part of sterris of heuene, and sente hem in to the erthe. And the dragoun stood bifore the womman, that was to berynge child, that whanne sche hadde borun child, he schulde deuoure hir sone.
5 Ta haifi ɗa, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al’ummai da sandar ƙarfe. Aka fyauce ɗanta zuwa wurin Allah da kuma kursiyinsa.
And sche bar a knaue child, that was to reulinge alle folkis in an yrun yerde; and hir sone was rauyschid to God, and to his trone.
6 Sai macen ta gudu zuwa hamada zuwa inda Allah ya shirya dominta, inda za a lura da ita har kwana 1,260.
And the womman flei in to wildirnesse, where sche hath a place maad redi of God, that he fede hir there a thousynde daies two hundrid and sixti.
7 Aka kuwa yi yaƙi a sama. Mika’ilu da mala’ikunsa yaƙi macijin, maciji da mala’ikunsa su ma suka mai da martani.
And a greet batel was maad in heuene, and Myyhel and hise aungels fouyten with the dragoun. And the dragoun fauyt, and hise aungels;
8 Amma macijin nan ba shi da isashen ƙarfi, har suka rasa matsayinsu a sama.
and thei hadden not myyt, nether the place of hem was foundun more in heuene.
9 Aka jefar da ƙaton jan macijin ƙasa, tsohon maciji nan da ake kira Iblis, ko Shaiɗan, wanda ya ɓad da dukan duniya. Aka jefar da shi ƙasa, tare da mala’ikunsa a duniya.
And thilke dragoun was cast doun, the greet elde serpent, that is clepid the Deuel, and Sathanas, that disseyueth al the world; he was cast doun in to the erthe, and hise aungels weren sent with hym.
10 Sa’an nan na ji babbar murya daga sama tana cewa, “Yanzu ceto da iko da mulkin Allahnmu, da kuma ikon Kiristinsa. Gama mai zargin’yan’uwanmu, wanda yake zarginsu a gaban Allahnmu dare da rana, an jefar da shi ƙasa.
And Y herde a greet vois in heuene, seiynge, Now is maad helthe, and vertu, and kyngdom of oure God, and the power of his Crist; for the accuser of oure britheren is cast doun, which accuside hem bifor the siyte of oure God dai and nyyt.
11 Sun ci nasara a kansa ta wurin jinin Ɗan Ragon da ta wurin kalmar shaidarsu; ba su ƙaunaci rayukansu sosai har da za su ja da baya daga mutuwa.
And thei ouercamen hym for the blood of the lomb, and for the word of his witnessing; and thei louyden not her lyues til to deth.
12 Saboda haka ku yi farin ciki, ku sammai, da ku da kuke zaune a cikinsu! Amma kaiton duniya da kuma teku, gama Iblis ya sauko gare ku! Ya cika da fushi, domin ya san cewa lokacinsa ya rage kaɗan.”
Therfor, ye heuenes, be ye glad, and ye that dwellen in hem. Wo to the erthe, and to the see; for the fend is come doun to you, and hath greet wraththe, witynge that he hath litil tyme.
13 Sa’ad da macijin ya ga an jefar da shi a duniya, sai ya fafari macen nan da ta haifi ɗa namiji.
And after that the dragoun sai, that he was cast doun to the erthe, he pursuede the womman, that bare the knaue child.
14 Sai aka ba wa macen fikafikai biyu na babban gaggafa, don ta tashi sama zuwa inda aka shirya mata a hamada, inda za a lura da ita na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci, inda macijin ba zai iya kaiwa ba.
And twei wengis of a greet egle weren youun to the womman, that sche schulde flee in to deseert, in to hir place, where sche is fed by tyme, and tymes, and half a tyme, fro the face of the serpent.
15 Sa’an nan daga bakinsa macijin ya kwarara ruwa kamar kogi, don ruwan ya cimma matan yă kuma kwashe ta tare da ambaliya.
And the serpent sente out of his mouth aftir the womman watir as a flood, that he schulde make hir to be drawun of the flood.
16 Amma ƙasa ta taimaki macen ta wurin buɗe bakinta ta kuma shanye ruwan kogin da macijin ya kwarara daga bakinsa.
And the erthe helpide the womman, and the erthe openyde his mouth, and soop up the flood, that the dragoun sente of his mouth.
17 Sai macijin ya yi fushi da macen ya kuma koma wajen sauran zuriyarta don yă yaƙe su waɗannan waɗanda suke biyayya da umarnan Allah suke kuma riƙe da shaidar Yesu.
And the dragoun was wrooth ayens the womman, and he wente to make batel with othere of hir seed, that kepen the maundementis of God, and han the witnessing of Jhesu Crist.

< Ru’uya ta Yohanna 12 >