< Ru’uya ta Yohanna 12 >
1 Babbar alama mai banmamaki ta bayyana a sama, mace tana lulluɓe da rana, da kuma wata a ƙarƙashin sawunta, akwai kuma rawani mai taurari goma sha biyu a kanta.
A great sign was seen in heaven: a woman clothed with the sun, and with the moon under her feet, and a crown of twelve stars was on her head.
2 Tana da ciki ta kuma yi kuka mai zafi yayinda take gab da haihuwa.
She was pregnant, and she was crying out in birth pains, in the anguish of childbirth.
3 Sai wata alama ta bayyana a sama, wani babban jan maciji mai kawuna bakwai da ƙahoni goma da rawani bakwai a kan kawunansa.
Then another sign was seen in heaven: Look! There was a huge red dragon that had seven heads and ten horns, and there were seven crowns on his heads.
4 Wutsiyarsa ta share kashi ɗaya bisa uku na taurari daga sararin sama ta kuma zubar da su ƙasa. Ƙaton jan macijin ya tsaya a gaban macen wadda take gab da haihuwa, don yă cinye ɗanta nan take bayan an haife shi.
His tail swept away a third of the stars in heaven and hurled them down to the earth. The dragon stood before the woman who was about to give birth, so that when she gave birth, he would devour her child.
5 Ta haifi ɗa, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al’ummai da sandar ƙarfe. Aka fyauce ɗanta zuwa wurin Allah da kuma kursiyinsa.
She gave birth to a son, a male child, who would rule all the nations with an iron rod. Her child was snatched away to God and to his throne,
6 Sai macen ta gudu zuwa hamada zuwa inda Allah ya shirya dominta, inda za a lura da ita har kwana 1,260.
and the woman fled into the wilderness, where God had prepared a place for her, so she could be taken care of for 1,260 days.
7 Aka kuwa yi yaƙi a sama. Mika’ilu da mala’ikunsa yaƙi macijin, maciji da mala’ikunsa su ma suka mai da martani.
Now there was war in heaven. Michael and his angels fought against the dragon; and the dragon and his angels fought back.
8 Amma macijin nan ba shi da isashen ƙarfi, har suka rasa matsayinsu a sama.
But the dragon was not strong enough to win. So there was no longer any place in heaven for him and his angels.
9 Aka jefar da ƙaton jan macijin ƙasa, tsohon maciji nan da ake kira Iblis, ko Shaiɗan, wanda ya ɓad da dukan duniya. Aka jefar da shi ƙasa, tare da mala’ikunsa a duniya.
The great dragon—that old serpent called the devil or Satan, who deceives the whole world—was thrown down to the earth, and his angels were thrown down with him.
10 Sa’an nan na ji babbar murya daga sama tana cewa, “Yanzu ceto da iko da mulkin Allahnmu, da kuma ikon Kiristinsa. Gama mai zargin’yan’uwanmu, wanda yake zarginsu a gaban Allahnmu dare da rana, an jefar da shi ƙasa.
Then I heard a loud voice in heaven: “Now have come the salvation and the power and the kingdom of our God, and the authority of his Christ. For the accuser of our brothers has been thrown down, the one who accused them before our God day and night.
11 Sun ci nasara a kansa ta wurin jinin Ɗan Ragon da ta wurin kalmar shaidarsu; ba su ƙaunaci rayukansu sosai har da za su ja da baya daga mutuwa.
They conquered him by the blood of the Lamb and by the word of their testimony, for they did not love their lives even to death.
12 Saboda haka ku yi farin ciki, ku sammai, da ku da kuke zaune a cikinsu! Amma kaiton duniya da kuma teku, gama Iblis ya sauko gare ku! Ya cika da fushi, domin ya san cewa lokacinsa ya rage kaɗan.”
Therefore rejoice you heavens, and all who reside in them! But woe to the earth and to the sea, because the devil has gone down to you! He is filled with terrible anger because he has only a little time!
13 Sa’ad da macijin ya ga an jefar da shi a duniya, sai ya fafari macen nan da ta haifi ɗa namiji.
When the dragon realized he had been thrown down to the earth, he pursued the woman who had given birth to the male child.
14 Sai aka ba wa macen fikafikai biyu na babban gaggafa, don ta tashi sama zuwa inda aka shirya mata a hamada, inda za a lura da ita na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci, inda macijin ba zai iya kaiwa ba.
But the woman was given the two wings of a great eagle, so that she would flee to the place prepared for her in the wilderness. This was the place where she would be taken care of, for a time, times, and half a time—out of the serpent's presence.
15 Sa’an nan daga bakinsa macijin ya kwarara ruwa kamar kogi, don ruwan ya cimma matan yă kuma kwashe ta tare da ambaliya.
The serpent poured water out of his mouth like a river, that he would make a flood to sweep her away.
16 Amma ƙasa ta taimaki macen ta wurin buɗe bakinta ta kuma shanye ruwan kogin da macijin ya kwarara daga bakinsa.
But the earth helped the woman. The earth opened its mouth and swallowed the river that the dragon was pouring out of his mouth.
17 Sai macijin ya yi fushi da macen ya kuma koma wajen sauran zuriyarta don yă yaƙe su waɗannan waɗanda suke biyayya da umarnan Allah suke kuma riƙe da shaidar Yesu.
Then the dragon was enraged at the woman and went off to wage war with the rest of her descendants, those who obey God's commandments and hold to the testimony about Jesus.