< Ru’uya ta Yohanna 12 >

1 Babbar alama mai banmamaki ta bayyana a sama, mace tana lulluɓe da rana, da kuma wata a ƙarƙashin sawunta, akwai kuma rawani mai taurari goma sha biyu a kanta.
A great sign appeared in the sky: a woman clothed with the sun, with the moon under her feet, and on her head a crown of twelve stars.
2 Tana da ciki ta kuma yi kuka mai zafi yayinda take gab da haihuwa.
And being pregnant she was crying out in labor, being in great pain to give birth.
3 Sai wata alama ta bayyana a sama, wani babban jan maciji mai kawuna bakwai da ƙahoni goma da rawani bakwai a kan kawunansa.
And another sign appeared in the sky: wow, a dragon, huge, fiery red, having seven heads and ten horns, with seven diadems on his heads.
4 Wutsiyarsa ta share kashi ɗaya bisa uku na taurari daga sararin sama ta kuma zubar da su ƙasa. Ƙaton jan macijin ya tsaya a gaban macen wadda take gab da haihuwa, don yă cinye ɗanta nan take bayan an haife shi.
And its tail grabbed a third of the stars of heaven and threw them to the earth. And the dragon stood before the woman who was about to give birth in order to devour her Child as soon as she gave birth.
5 Ta haifi ɗa, namiji, wanda zai yi mulkin dukan al’ummai da sandar ƙarfe. Aka fyauce ɗanta zuwa wurin Allah da kuma kursiyinsa.
And she bore a Son, a male, who would shepherd all the nations with a rod of iron. And her Child was snatched up to God, even to His throne.
6 Sai macen ta gudu zuwa hamada zuwa inda Allah ya shirya dominta, inda za a lura da ita har kwana 1,260.
And the woman fled into the wilderness to where she has a place prepared by God, so that they may nourish her there one thousand two hundred and sixty days.
7 Aka kuwa yi yaƙi a sama. Mika’ilu da mala’ikunsa yaƙi macijin, maciji da mala’ikunsa su ma suka mai da martani.
War was declared in heaven; Michael and his angels were to wage war with the dragon; so the dragon and his angels made war,
8 Amma macijin nan ba shi da isashen ƙarfi, har suka rasa matsayinsu a sama.
but he was not strong enough; neither was there any place found for him in heaven any more.
9 Aka jefar da ƙaton jan macijin ƙasa, tsohon maciji nan da ake kira Iblis, ko Shaiɗan, wanda ya ɓad da dukan duniya. Aka jefar da shi ƙasa, tare da mala’ikunsa a duniya.
So the great dragon was expelled, that ancient serpent, who is called Slanderer and Satan, who deceives the whole inhabited world; he was thrown into the earth, and his angels were expelled with him.
10 Sa’an nan na ji babbar murya daga sama tana cewa, “Yanzu ceto da iko da mulkin Allahnmu, da kuma ikon Kiristinsa. Gama mai zargin’yan’uwanmu, wanda yake zarginsu a gaban Allahnmu dare da rana, an jefar da shi ƙasa.
And I heard a loud voice in the heaven saying: “Now the salvation and the power have come, even the Kingdom of our God and the authority of His Christ, because the accuser of our brothers has been thrown down, who accused them before our God day and night.
11 Sun ci nasara a kansa ta wurin jinin Ɗan Ragon da ta wurin kalmar shaidarsu; ba su ƙaunaci rayukansu sosai har da za su ja da baya daga mutuwa.
And they conquered him by the blood of the Lamb and by the word of their testimony, and they did not cherish their lives, even up to death.
12 Saboda haka ku yi farin ciki, ku sammai, da ku da kuke zaune a cikinsu! Amma kaiton duniya da kuma teku, gama Iblis ya sauko gare ku! Ya cika da fushi, domin ya san cewa lokacinsa ya rage kaɗan.”
Therefore rejoice, O heavens, yes, you who are dwelling in them! Woe to the earth and the sea! Because the devil has come down to you, having great wrath, knowing that he has little time.”
13 Sa’ad da macijin ya ga an jefar da shi a duniya, sai ya fafari macen nan da ta haifi ɗa namiji.
So when the dragon perceived that he had been thrown into the earth, he persecuted the woman who gave birth to the Male.
14 Sai aka ba wa macen fikafikai biyu na babban gaggafa, don ta tashi sama zuwa inda aka shirya mata a hamada, inda za a lura da ita na ɗan lokaci, lokuta da rabin lokaci, inda macijin ba zai iya kaiwa ba.
And to the woman were given two wings of the great eagle, so that she might fly into the wilderness, into her place, so that she might be nourished there for a time and times and half a time, from the presence of the serpent.
15 Sa’an nan daga bakinsa macijin ya kwarara ruwa kamar kogi, don ruwan ya cimma matan yă kuma kwashe ta tare da ambaliya.
So the serpent expelled water from his mouth after the woman, like a river, so as to cause her to be overwhelmed by the flood.
16 Amma ƙasa ta taimaki macen ta wurin buɗe bakinta ta kuma shanye ruwan kogin da macijin ya kwarara daga bakinsa.
But the ground helped the woman; indeed, the ground opened its mouth and drank up the river that the dragon expelled from his mouth.
17 Sai macijin ya yi fushi da macen ya kuma koma wajen sauran zuriyarta don yă yaƙe su waɗannan waɗanda suke biyayya da umarnan Allah suke kuma riƙe da shaidar Yesu.
So the dragon was furious about the woman and off he went to make war with the rest of her offspring, those who keep the commands of God and hold the testimony of Jesus.

< Ru’uya ta Yohanna 12 >