< Ru’uya ta Yohanna 11 >

1 Aka ba ni ƙara kamar sandan awo aka kuma ce mini, “Tafi ka auna haikalin Allah da bagaden, ka kuma ƙirga waɗanda suke sujada a can.
Etu pichete, ekta patla lathi nisena moike naap kori bole nimite dise. Moike koise, “Uthibi aru Isor laga mondoli aru bedi laga naap lobi, aru kun manu ta te aradhana kore taikhan laga bhi naap lobi.
2 Sai dai kada ka haɗa da harabar waje; kada ka auna ta, domin an ba da ita ga Al’ummai. Za su tattaka birni mai tsarki har watanni 42.
Kintu mondoli laga bahar jaga to naap nolobi, etu to Porjati manu khan ke di dise. Taikhan etu pobitro sheher Jerusalem ke tin saal adha tak theng pora chipa bo.
3 Zan kuma ba wa shaiduna nan biyu iko, za su kuwa yi annabci na kwanaki 1,260, saye da gwadon makoki.”
Aru Moi laga duita gawahi khan ke adhikar dibo, aru taikhan 1,260 din tak bhabobani kobo, bosta laga kapra lagai kene.”
4 Waɗannan su ne itatuwan zaitun biyu da kuma alkukai biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
Etu duita oliv ghas aru duita saaki jola laga khuri ase juntu prithibi laga Probhu usorte khara ase.
5 Duk wanda ya yi ƙoƙari yin musu lahani, wuta za tă fito daga bakunansu ta cinye abokan gābansu. Haka ne duk mai niyyar yin musu lahani zai mutu.
Kunba manu etu ke nuksan kori bole kosis korile, taikhan laga mukh para jui ulaikene dushman khan ke khotom kori dibo.
6 Waɗannan mutane suna da iko su kulle sararin sama don kada a yi ruwan sama a lokacin da suke annabci; suna kuma da iko su juye ruwaye su zama jini su kuma bugi duniya da kowace irin annoba a duk lokacin da suke so.
Taikhan logote akas to bondh kori bole adhikar ase kelemane jitia taikhan bhabobani kobo etu homoi te pani nagiribo. Taikhan logote pani ke khun bonai dibole takot ase aru etu prithibi te alag kisim laga dukh aru bemar pora bhorta kori bole nimite taikhan logote adhikar ase.
7 To, da suka gama shaidarsu, dabbar da takan fito daga Abis za tă kai musu hari, tă kuwa sha ƙarfinsu tă kuma kashe su. (Abyssos g12)
Jitia taikhan laga gawahi kora to khotom hobo, etu khotom nakora mati nichete thaka janwar taikhan uporte lorai koribo. Taikhan ke morai dikene sob jiti lobo. (Abyssos g12)
8 Gawawwakinsu za su kasance a kwance a titin babban birni, wanda a misalce ake kira Sodom da Masar, inda kuma aka gicciye Ubangijinsu.
Taikhan laga mora gaw to dangor sheher laga rasta te giri thakibo -kuntu ke Sodom aru Egypt koi- jun jagate taikhan laga Probhu ke Cross te mari disele.
9 Kwana uku da rabi mutane daga kowace jama’a, kabila, harshe da kuma al’umma za su yi ta kallon gawawwakinsu su kuma ƙi binne su.
Aru tin din adha tak sob jati, desh aru alag kotha kowa manu khan taikhan laga mora gaw to sabo aru taikhan laga gaw to kobor te hali bole nimite nadibo.
10 Mazaunan duniya za su ƙyaface su kuma yi biki ta wurin aika kyautai wa juna, domin waɗannan annabawan nan biyu ne suka azabtar da mazaunan duniya.
Aru kiman manu etu prithibi te ase, taikhan etu dikhi kene khushi koribo. Taikhan ekjon-ekjon ke uphar dikene duita bhabobadi khan kun duniya te thakise etu naam pora khushi koribo.
11 Amma bayan kwana uku da rabi ɗin numfashin rai daga Allah ya shige su, suka kuwa tashi tsaye, tsoro kuma ya kama waɗanda suka gan su.
Kintu tin din adha pichete Isor laga saas to taikhan uporte di dibo, aru taikhan laga theng te khara hobo aru kun manu etu dikhibo taikhan bisi bhoi koribo.
12 Sai suka ji wata babbar murya daga sama tana ce musu, “Ku hauro nan.” Suka kuwa haura zuwa sama cikin girgije, yayinda abokan gābansu suna kallo.
Titia sorgo pora dangor awaj pora taikhan ke koi thaka hunibo, “Yate uporte ahibi!” Titia taikhan badal pora sorgote jai jabo, aru taikhan laga dushman khan sai thakibo.
13 A wannan sa’a aka yi wata babbar girgizar ƙasa kashi ɗaya bisa goma kuma na birnin ya rushe. Aka kashe mutane dubu bakwai a girgizar ƙasar, waɗanda suka tsira kuwa suka ji tsoro suka ɗaukaka Allah na sama.
Thik etu homoi te, mati dangor pora hili bo, aru sheher laga dos bhag khotom hoi jabo. Sat-ta hajar manu etu homoi te moribo, aru kun manu bachi jai taikhan bhoi lagibo aru etu dikhi kene Isor ke mohima dibo.
14 Kaito na biyu ya wuce; kaito na uku yana zuwa ba da daɗewa ba.
Aru dusra hai kotha bhi paar hoise. Sabi! Tisra hai kotha to joldi ahi ase.
15 Mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji muryoyi masu ƙarfi a sama da suka ce, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Kiristinsa, zai kuwa yi mulki har abada abadin.” (aiōn g165)
Titia sat-ta sorgodoth pora tai laga bhigul bajaise, aru sorgote dangor awaj khan pora koise, “Etu duniya laga rajyo to Probhu aru Khrista laga rajyo hoise, Aru Tai hodai nimite raj koribo.” (aiōn g165)
16 Sai dattawan nan ashirin da huɗu da suke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa suka kuma yi wa Allah sujada,
Titia choubees bura manu khan, kun Isor laga usorte singhason te bohi ase taikhan laga matha niche kori kene Isor ke aradhana koribo.
17 suna cewa, “Muna maka godiya ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki, wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā, domin ka karɓi ikonka mai girma ka kuma fara mulki.
Taikhan koise, “Moi khan Apuni ke dhanyavad di ase, Mohan Probhu Isor, kun thakise, aru hodai ase, Apuni dangor takot to loi loise aru raj korise.
18 Al’ummai suka yi fushi; fushinka kuwa ya zo. Lokaci ya yi don a shari’anta matattu, da kuma don sākawa wa bayinka annabawa da tsarkakanka da kuma su waɗanda suke girmama sunanka, ƙarami da babba, don kuma hallakar da waɗanda suka hallaka duniya.”
Etu desh khan khong uthise, Kintu Apuni laga khong to ahise, Aru mora manu khan ke bisar kori bole nimite, Aru Apuni laga noukar khan ke inam dibole nimite, Bhabobadi aru pobitro manu khan ke inam dibole nimite, Aru kun manu apuni laga naam te bhoi kori kene thake, Chutu aru dangor, Aru kun manu etu prithibi to khotom kore taikhan ke khotom kori dibole nimite.”
19 Sa’an nan aka buɗe haikalin Allah da yake a sama, kuma a cikin haikalinsa aka ga akwatin alkawarinsa. Sai kuwa ga walƙiya, ƙararraki, tsawa, girgizar ƙasa, da kuma ƙanƙara masu girma.
Titia sorgote thaka mondoli to khuli jaise aru Probhu laga vachan laga ark to tai laga mondoli majote dikhise. Etu homoi te dangor bhijili ujala ahise, jor pora hala kori kene, aru mati hili se aru dangor pathor khan girise.

< Ru’uya ta Yohanna 11 >