< Ru’uya ta Yohanna 11 >

1 Aka ba ni ƙara kamar sandan awo aka kuma ce mini, “Tafi ka auna haikalin Allah da bagaden, ka kuma ƙirga waɗanda suke sujada a can.
[An angel gave] to me a reed similar to a measuring stick. He said [to me], “[Christ says this: ‘Go] to the temple [where people worship] God, measure it and the altar [in it], and count the people who worship there.
2 Sai dai kada ka haɗa da harabar waje; kada ka auna ta, domin an ba da ita ga Al’ummai. Za su tattaka birni mai tsarki har watanni 42.
But do not measure the courtyard outside [of the temple] [DOU], because [it] has been given {[God] has given it} to [the] non-Jewish [people. As a result], they will trample [Jerusalem city] for 42 months.
3 Zan kuma ba wa shaiduna nan biyu iko, za su kuwa yi annabci na kwanaki 1,260, saye da gwadon makoki.”
I will appoint my two (witnesses/men who will tell others about me). They will proclaim what I reveal to them for 1,260 days. They will wear [rough] clothes made from goat’s hair [to show that they are sad about people’s sin].’”
4 Waɗannan su ne itatuwan zaitun biyu da kuma alkukai biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
Those [witnesses are the ones] that are represented by the two olive trees and the two lampstands that are in the presence of the Lord [who rules] the earth [SYM].
5 Duk wanda ya yi ƙoƙari yin musu lahani, wuta za tă fito daga bakunansu ta cinye abokan gābansu. Haka ne duk mai niyyar yin musu lahani zai mutu.
If enemies try to harm those [witnesses], fire will come from the mouths of the witnesses and destroy them. If people want to harm them, [the two witnesses] will certainly kill them similarly.
6 Waɗannan mutane suna da iko su kulle sararin sama don kada a yi ruwan sama a lokacin da suke annabci; suna kuma da iko su juye ruwaye su zama jini su kuma bugi duniya da kowace irin annoba a duk lokacin da suke so.
Those [witnesses] will have authority to keep rain from falling during the time that they are proclaiming what God reveals to them. They also will have authority to cause water [everywhere] to become [red like] [MET] blood, and [authority] to cause all kinds of plagues to occur. They will do this as often as they want to.
7 To, da suka gama shaidarsu, dabbar da takan fito daga Abis za tă kai musu hari, tă kuwa sha ƙarfinsu tă kuma kashe su. (Abyssos g12)
When they have finished proclaiming [to people the message from God], the beast that comes up (from the underworld/from the deep dark pit) will attack them, overcome them, and kill them. (Abyssos g12)
8 Gawawwakinsu za su kasance a kwance a titin babban birni, wanda a misalce ake kira Sodom da Masar, inda kuma aka gicciye Ubangijinsu.
The dead bodies of the [two] witnesses will lie in the street of the great city where their Lord was crucified, the city that is symbolically named Sodom or Egypt [because its people are very evil, like the people who lived in Sodom and Egypt].
9 Kwana uku da rabi mutane daga kowace jama’a, kabila, harshe da kuma al’umma za su yi ta kallon gawawwakinsu su kuma ƙi binne su.
Individuals of many people-[groups], tribes, language [groups] [MTY], and nations will look at their dead bodies for three and a half days. But these individuals will not allow [anyone] to bury their bodies.
10 Mazaunan duniya za su ƙyaface su kuma yi biki ta wurin aika kyautai wa juna, domin waɗannan annabawan nan biyu ne suka azabtar da mazaunan duniya.
When the [rebellious] people who live on the earth [see that the witnesses are dead], they will rejoice and celebrate. They will send gifts to each other, because these two prophets had [caused plagues to occur which] tormented the [rebellious] people on the earth.
11 Amma bayan kwana uku da rabi ɗin numfashin rai daga Allah ya shige su, suka kuwa tashi tsaye, tsoro kuma ya kama waɗanda suka gan su.
But after three and a half days, God will cause those two witnesses to breathe again and live. They will stand up, and those who see them will be terrified.
12 Sai suka ji wata babbar murya daga sama tana ce musu, “Ku hauro nan.” Suka kuwa haura zuwa sama cikin girgije, yayinda abokan gābansu suna kallo.
The [two witnesses] will hear a loud voice which came from heaven saying to them: “Come up here!” Then they will go up to heaven in a cloud. Their enemies will see them [as they ascend].
13 A wannan sa’a aka yi wata babbar girgizar ƙasa kashi ɗaya bisa goma kuma na birnin ya rushe. Aka kashe mutane dubu bakwai a girgizar ƙasar, waɗanda suka tsira kuwa suka ji tsoro suka ɗaukaka Allah na sama.
At that same time there will be a terrible earthquake, which will cause a tenth of [the buildings in] [MTY] the city will collapse, and 7,000 people will die. The rest of the people will be afraid and [acknowledge] that the God [who rules in] heaven is awesome.
14 Kaito na biyu ya wuce; kaito na uku yana zuwa ba da daɗewa ba.
That will be the second terrible event. [Be aware that] the third tragic event will happen soon.
15 Mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji muryoyi masu ƙarfi a sama da suka ce, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Kiristinsa, zai kuwa yi mulki har abada abadin.” (aiōn g165)
Then the seventh angel blew [his trumpet]. Angels in heaven shouted loudly, “Our Lord [God] and the Messiah [whom he has appointed] can now govern [everyone in] [MTY] the world, and they will continue to rule people forever!” (aiōn g165)
16 Sai dattawan nan ashirin da huɗu da suke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa suka kuma yi wa Allah sujada,
The 24 elders who sit on their thrones in God’s presence (prostrated themselves/bowed down low) and worshipped him.
17 suna cewa, “Muna maka godiya ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki, wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā, domin ka karɓi ikonka mai girma ka kuma fara mulki.
They said: Lord God, you are the Almighty One! You are the one who exists now! You are the one who has always existed! We thank you that you have defeated by your power everyone who has rebelled against you, and you now rule over everyone in the world.
18 Al’ummai suka yi fushi; fushinka kuwa ya zo. Lokaci ya yi don a shari’anta matattu, da kuma don sākawa wa bayinka annabawa da tsarkakanka da kuma su waɗanda suke girmama sunanka, ƙarami da babba, don kuma hallakar da waɗanda suka hallaka duniya.”
The unbelieving people of [MTY] the nations were raging at you. As a result you have become very angry with them. You have decided that this is the appropriate time for you to judge all the dead people. You have also decided that it is the time for you to reward all your servants, both the prophets and the rest of your people who reverence you [MTY], whether they were considered socially significant/important or socially insignificant/unimportant. It is time for you to reward all of them! You have also decided it is the time for you to destroy the people who are destroying others on the earth.
19 Sa’an nan aka buɗe haikalin Allah da yake a sama, kuma a cikin haikalinsa aka ga akwatin alkawarinsa. Sai kuwa ga walƙiya, ƙararraki, tsawa, girgizar ƙasa, da kuma ƙanƙara masu girma.
Then God’s temple in heaven was opened {was open} and [I] saw in the temple the sacred box/chest that contains God’s commandments. Lightning was flashing, it was thundering and rumbling, the earth shook, and large hailstones [fell from the sky].

< Ru’uya ta Yohanna 11 >