< Ru’uya ta Yohanna 11 >

1 Aka ba ni ƙara kamar sandan awo aka kuma ce mini, “Tafi ka auna haikalin Allah da bagaden, ka kuma ƙirga waɗanda suke sujada a can.
And there was given unto me a reed, like unto a staff, saying—Rise, and measure the Sanctuary of God, and the altar, and them who are doing homage therein;
2 Sai dai kada ka haɗa da harabar waje; kada ka auna ta, domin an ba da ita ga Al’ummai. Za su tattaka birni mai tsarki har watanni 42.
and, the court that is outside the Sanctuary, cast thou outside, and do not measure, it, because it hath been given unto the nations, and, the holy city, shall they tread under foot, forty and two months.
3 Zan kuma ba wa shaiduna nan biyu iko, za su kuwa yi annabci na kwanaki 1,260, saye da gwadon makoki.”
And I will give unto my two witnesses, that they shall prophesy, a thousand two hundred and sixty days, arrayed in sackcloth.
4 Waɗannan su ne itatuwan zaitun biyu da kuma alkukai biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
These, are the two olive-trees, and the two lamps, which, before the Lord of the earth, do stand.
5 Duk wanda ya yi ƙoƙari yin musu lahani, wuta za tă fito daga bakunansu ta cinye abokan gābansu. Haka ne duk mai niyyar yin musu lahani zai mutu.
And, if any one, upon them, chooseth to inflict injury, fire, cometh forth out of their mouth, and devoureth their enemies; and, if anyone shall choose, upon them, to inflict injury, thus, must he be slain.
6 Waɗannan mutane suna da iko su kulle sararin sama don kada a yi ruwan sama a lokacin da suke annabci; suna kuma da iko su juye ruwaye su zama jini su kuma bugi duniya da kowace irin annoba a duk lokacin da suke so.
These, have authority to shut heaven, in order that, no rain, be moistening in the days of their prophesying; and, authority, have they, over the waters, to be turning them into blood, and to smite the land, with any manner of plague, as often as they will.
7 To, da suka gama shaidarsu, dabbar da takan fito daga Abis za tă kai musu hari, tă kuwa sha ƙarfinsu tă kuma kashe su. (Abyssos g12)
And, as soon as they have completed their witnessing, the wild-beast that is to come up out of the abyss, will make war with them, and overcome them, and slay them. (Abyssos g12)
8 Gawawwakinsu za su kasance a kwance a titin babban birni, wanda a misalce ake kira Sodom da Masar, inda kuma aka gicciye Ubangijinsu.
And their dead bodies [lie] upon the broadway of the great city, the which is called, spiritually, Sodom and Egypt, where, their Lord also was crucified.
9 Kwana uku da rabi mutane daga kowace jama’a, kabila, harshe da kuma al’umma za su yi ta kallon gawawwakinsu su kuma ƙi binne su.
And [some] of the peoples, and tribes, and tongues, and nations, see, their dead bodies three days and a half, and, their dead bodies, do they not suffer to be put into a tomb.
10 Mazaunan duniya za su ƙyaface su kuma yi biki ta wurin aika kyautai wa juna, domin waɗannan annabawan nan biyu ne suka azabtar da mazaunan duniya.
And, they who are dwelling upon the earth, rejoice over them, and make merry, and, gifts, will they send one to another, —because, these two prophets, tormented them that were dwelling upon the earth.
11 Amma bayan kwana uku da rabi ɗin numfashin rai daga Allah ya shige su, suka kuwa tashi tsaye, tsoro kuma ya kama waɗanda suka gan su.
And, after [the] three days and a half, a spirit of life from God, entered within them, and they stood upon their feet; and, great fear, fell upon them who were beholding them.
12 Sai suka ji wata babbar murya daga sama tana ce musu, “Ku hauro nan.” Suka kuwa haura zuwa sama cikin girgije, yayinda abokan gābansu suna kallo.
And they heard a loud voice out of heaven, saying unto them—Come up hither! And they went up into heaven, in the cloud, and, their enemies, beheld them.
13 A wannan sa’a aka yi wata babbar girgizar ƙasa kashi ɗaya bisa goma kuma na birnin ya rushe. Aka kashe mutane dubu bakwai a girgizar ƙasar, waɗanda suka tsira kuwa suka ji tsoro suka ɗaukaka Allah na sama.
And, in that hour, there came to be a great earthquake; and, the tenth of the city, fell, and there were slain, in the earthquake, names of men—seven thousand. And, the rest, became, greatly afraid, and gave glory unto the God of heaven.
14 Kaito na biyu ya wuce; kaito na uku yana zuwa ba da daɗewa ba.
The second Woe, hath passed away, —lo! the third Woe, cometh speedily.
15 Mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji muryoyi masu ƙarfi a sama da suka ce, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Kiristinsa, zai kuwa yi mulki har abada abadin.” (aiōn g165)
And, the seventh messenger, sounded; and there came to be loud voices in heaven, saying—The kingdom of the world, hath become [the kingdom] of our Lord and of his Christ, and he shall reign unto the ages of ages. (aiōn g165)
16 Sai dattawan nan ashirin da huɗu da suke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa suka kuma yi wa Allah sujada,
And, the twenty-four elders who, before God, do sit upon their thrones, fell down upon their faces, and rendered homage unto God,
17 suna cewa, “Muna maka godiya ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki, wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā, domin ka karɓi ikonka mai girma ka kuma fara mulki.
saying—We give thanks unto thee, O Lord God, the Almighty, Who is, and Who was; because thou hast taken thy great power, and hast become king.
18 Al’ummai suka yi fushi; fushinka kuwa ya zo. Lokaci ya yi don a shari’anta matattu, da kuma don sākawa wa bayinka annabawa da tsarkakanka da kuma su waɗanda suke girmama sunanka, ƙarami da babba, don kuma hallakar da waɗanda suka hallaka duniya.”
And, the nations, were angered; and thine anger, came, and the fit time of the dead, to be vindicated, and to give their reward unto thy servants the prophets, and unto the saints, and unto them who revere thy name—the small and the great, and to despoil them who were despoiling the earth.
19 Sa’an nan aka buɗe haikalin Allah da yake a sama, kuma a cikin haikalinsa aka ga akwatin alkawarinsa. Sai kuwa ga walƙiya, ƙararraki, tsawa, girgizar ƙasa, da kuma ƙanƙara masu girma.
And the sanctuary of God which is in heaven, was opened, and the ark of his covenant in his sanctuary, appeared, and there came to be lightnings, and voices, and thunderings, and an earthquake, and great hail.

< Ru’uya ta Yohanna 11 >