< Ru’uya ta Yohanna 11 >
1 Aka ba ni ƙara kamar sandan awo aka kuma ce mini, “Tafi ka auna haikalin Allah da bagaden, ka kuma ƙirga waɗanda suke sujada a can.
I was given a measuring rod and told, “Get up and measure the Temple of God, and the altar, and count those who are worshiping there.
2 Sai dai kada ka haɗa da harabar waje; kada ka auna ta, domin an ba da ita ga Al’ummai. Za su tattaka birni mai tsarki har watanni 42.
Don't measure the court outside the Temple, leave that, because it has been handed over to the nations. They will trample down the holy city for forty-two months.
3 Zan kuma ba wa shaiduna nan biyu iko, za su kuwa yi annabci na kwanaki 1,260, saye da gwadon makoki.”
I will give my two witnesses power, and they will prophesy 1,260 days, dressed in sackcloth.”
4 Waɗannan su ne itatuwan zaitun biyu da kuma alkukai biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
They are the two olive trees and the two candlesticks that stand in front of the Lord of the earth.
5 Duk wanda ya yi ƙoƙari yin musu lahani, wuta za tă fito daga bakunansu ta cinye abokan gābansu. Haka ne duk mai niyyar yin musu lahani zai mutu.
If anyone tries to harm them, fire comes out of their mouths and burns up their enemies. This is how anyone who tries to harm them will be killed.
6 Waɗannan mutane suna da iko su kulle sararin sama don kada a yi ruwan sama a lokacin da suke annabci; suna kuma da iko su juye ruwaye su zama jini su kuma bugi duniya da kowace irin annoba a duk lokacin da suke so.
These two witnesses have the power to close the sky so that it will not rain during the time of their prophecy. They also have the power to turn the waters into blood, and to strike the earth with all kinds of plagues, as often as they want.
7 To, da suka gama shaidarsu, dabbar da takan fito daga Abis za tă kai musu hari, tă kuwa sha ƙarfinsu tă kuma kashe su. (Abyssos )
When they finish their testimony, the beast coming from the Abyss will attack them, defeat them, and kill them. (Abyssos )
8 Gawawwakinsu za su kasance a kwance a titin babban birni, wanda a misalce ake kira Sodom da Masar, inda kuma aka gicciye Ubangijinsu.
Their dead bodies will lie on the open street of the great city, called Sodom and Egypt in spiritual symbolism—also the place where their Lord was crucified.
9 Kwana uku da rabi mutane daga kowace jama’a, kabila, harshe da kuma al’umma za su yi ta kallon gawawwakinsu su kuma ƙi binne su.
For three and a half days those from the peoples and tribes and languages and nations will look at their dead bodies, and will not allow their corpses to be buried.
10 Mazaunan duniya za su ƙyaface su kuma yi biki ta wurin aika kyautai wa juna, domin waɗannan annabawan nan biyu ne suka azabtar da mazaunan duniya.
The inhabitants of the earth are delighted they are dead, and celebrate, sending gifts to each other, because these two prophets had been a torment to them.
11 Amma bayan kwana uku da rabi ɗin numfashin rai daga Allah ya shige su, suka kuwa tashi tsaye, tsoro kuma ya kama waɗanda suka gan su.
But three and half days later God's life-giving breath entered them and they stood on their feet. Those who saw this were absolutely terrified.
12 Sai suka ji wata babbar murya daga sama tana ce musu, “Ku hauro nan.” Suka kuwa haura zuwa sama cikin girgije, yayinda abokan gābansu suna kallo.
The two witnesses heard a loud voice from heaven telling them, “Come up here!” So they ascended to heaven in a cloud while their enemies watched.
13 A wannan sa’a aka yi wata babbar girgizar ƙasa kashi ɗaya bisa goma kuma na birnin ya rushe. Aka kashe mutane dubu bakwai a girgizar ƙasar, waɗanda suka tsira kuwa suka ji tsoro suka ɗaukaka Allah na sama.
At the same time there was a huge earthquake, and one tenth of the city collapsed. Seven thousand people were killed in the earthquake, and the rest were terrified, and gave glory to the God of heaven.
14 Kaito na biyu ya wuce; kaito na uku yana zuwa ba da daɗewa ba.
The second Disaster is over; the third Disaster is about to arrive!
15 Mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji muryoyi masu ƙarfi a sama da suka ce, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Kiristinsa, zai kuwa yi mulki har abada abadin.” (aiōn )
The seventh angel blew his trumpet, and loud voices shouted in heaven, “The kingdom of the world has become the kingdom of our Lord, and of his Christ, and he shall reign for ever and ever.” (aiōn )
16 Sai dattawan nan ashirin da huɗu da suke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa suka kuma yi wa Allah sujada,
The twenty-four elders who sit on their thrones in God's presence fell down on their faces and worshipped God.
17 suna cewa, “Muna maka godiya ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki, wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā, domin ka karɓi ikonka mai girma ka kuma fara mulki.
They said, “We thank you, Lord God, the All-powerful One, who is and was, because you have taken up your great power and have asserted your rule.”
18 Al’ummai suka yi fushi; fushinka kuwa ya zo. Lokaci ya yi don a shari’anta matattu, da kuma don sākawa wa bayinka annabawa da tsarkakanka da kuma su waɗanda suke girmama sunanka, ƙarami da babba, don kuma hallakar da waɗanda suka hallaka duniya.”
The nations became furious, but your judgment has come, the time when the dead will be judged. This is the time when your servants the prophets and the believers will be given their reward, those who respect your authority, both the weak and the powerful. This is also the time when you will destroy those who destroy the earth.
19 Sa’an nan aka buɗe haikalin Allah da yake a sama, kuma a cikin haikalinsa aka ga akwatin alkawarinsa. Sai kuwa ga walƙiya, ƙararraki, tsawa, girgizar ƙasa, da kuma ƙanƙara masu girma.
Then the Temple of God in heaven was opened, and the Ark of the Agreement could be seen inside his Temple. There were lightning flashes, the sound of thunder, an earthquake, and a great hailstorm.