< Ru’uya ta Yohanna 11 >

1 Aka ba ni ƙara kamar sandan awo aka kuma ce mini, “Tafi ka auna haikalin Allah da bagaden, ka kuma ƙirga waɗanda suke sujada a can.
I dána mi třtina, podobná prutu, a postavil se tu anděl, a řekl mi: Vstaň, a změř chrám Boží, i oltář, i ty, kteříž se modlí v něm.
2 Sai dai kada ka haɗa da harabar waje; kada ka auna ta, domin an ba da ita ga Al’ummai. Za su tattaka birni mai tsarki har watanni 42.
Ale síň, kteráž vně jest, vyvrz ven, a neměř jí. Neboť jest dána pohanům, a budouť tlačiti město svaté za čtyřidceti a dva měsíce.
3 Zan kuma ba wa shaiduna nan biyu iko, za su kuwa yi annabci na kwanaki 1,260, saye da gwadon makoki.”
Ale dám jej dvěma svědkům svým, kteříž budou prorokovati tisíc dvě stě a šedesáte dnů, oblečeni jsouce v pytle.
4 Waɗannan su ne itatuwan zaitun biyu da kuma alkukai biyu da suke tsaye a gaban Ubangijin duniya.
Tiť jsou dvě olivy a dva svícnové, stojící před obličejem Boha Pána vší země.
5 Duk wanda ya yi ƙoƙari yin musu lahani, wuta za tă fito daga bakunansu ta cinye abokan gābansu. Haka ne duk mai niyyar yin musu lahani zai mutu.
Jimžto jestliže by kdo chtěl ubližovati, oheň vyjde z úst jejich, a sžíře nepřátely jejich; a takť musí zabit býti, kdož by koli jim škoditi chtěl.
6 Waɗannan mutane suna da iko su kulle sararin sama don kada a yi ruwan sama a lokacin da suke annabci; suna kuma da iko su juye ruwaye su zama jini su kuma bugi duniya da kowace irin annoba a duk lokacin da suke so.
Tiť mají moc zavříti nebe, aby nepršel déšť za dnů proroctví jejich; a mají moc nad vodami, obrátiti je v krev, a bíti zemi všelikou ranou, kolikrát by koli chtěli.
7 To, da suka gama shaidarsu, dabbar da takan fito daga Abis za tă kai musu hari, tă kuwa sha ƙarfinsu tă kuma kashe su. (Abyssos g12)
Ale když dokonají svědectví své, šelma vystupující z propasti válku povede proti nim, a zvítězí nad nimi, i zmorduje je. (Abyssos g12)
8 Gawawwakinsu za su kasance a kwance a titin babban birni, wanda a misalce ake kira Sodom da Masar, inda kuma aka gicciye Ubangijinsu.
A ležeti budou těla jejich mrtvá na ryncích města velikého, kteréž slove duchovně Sodoma a Egypt, kdežto i Pán náš ukřižován jest.
9 Kwana uku da rabi mutane daga kowace jama’a, kabila, harshe da kuma al’umma za su yi ta kallon gawawwakinsu su kuma ƙi binne su.
A vídati budou mnozí z pokolení, a z lidu, a z jazyků, i z národů těla jejich mrtvá za půl čtvrta dne, ale těl jejich mrtvých nedadí pochovati v hrobích.
10 Mazaunan duniya za su ƙyaface su kuma yi biki ta wurin aika kyautai wa juna, domin waɗannan annabawan nan biyu ne suka azabtar da mazaunan duniya.
Anobrž ti, kteříž přebývají na zemi, radovati se budou nad nimi a veseliti se, a dary budou posílati jedni druhým; nebo ti dva proroci trápili ty, jenž přebývají na zemi.
11 Amma bayan kwana uku da rabi ɗin numfashin rai daga Allah ya shige su, suka kuwa tashi tsaye, tsoro kuma ya kama waɗanda suka gan su.
Ale po půl čtvrtu dni duch života od Boha poslaný vstoupil do nich, i postavili se na nohách svých, a bázeň veliká spadla na ty, kteříž je viděli.
12 Sai suka ji wata babbar murya daga sama tana ce musu, “Ku hauro nan.” Suka kuwa haura zuwa sama cikin girgije, yayinda abokan gābansu suna kallo.
Potom slyšeli hlas veliký s nebe, řkoucí k nim: Vstupte sem! I vstoupili na nebe v oblace, a hleděli na ně nepřátelé jejich.
13 A wannan sa’a aka yi wata babbar girgizar ƙasa kashi ɗaya bisa goma kuma na birnin ya rushe. Aka kashe mutane dubu bakwai a girgizar ƙasar, waɗanda suka tsira kuwa suka ji tsoro suka ɗaukaka Allah na sama.
A v tu hodinu stalo se země třesení veliké, a desátý díl města padl, a zbito jest v tom země třesení sedm tisíců lidu, a jiní zstrašeni jsou, a vzdali slávu Bohu nebeskému.
14 Kaito na biyu ya wuce; kaito na uku yana zuwa ba da daɗewa ba.
Bída druhá pominula, a aj, třetí bída přijde rychle.
15 Mala’ika na bakwai ya busa ƙahonsa, sai aka ji muryoyi masu ƙarfi a sama da suka ce, “Mulkin duniya ya zama mulkin Ubangijinmu da na Kiristinsa, zai kuwa yi mulki har abada abadin.” (aiōn g165)
A sedmý anděl zatroubil, i stali se hlasové velicí v nebi, řkoucí: Učiněnať jsou království všeho světa Pána našeho a Krista jeho, a kralovatiť bude na věky věků. (aiōn g165)
16 Sai dattawan nan ashirin da huɗu da suke zaune a kursiyoyinsu a gaban Allah, suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa suka kuma yi wa Allah sujada,
Tedy těch čtyřmecítma starců, kteříž před obličejem Božím sedí na stolicích svých, padli na tváři své, a klaněli se Bohu,
17 suna cewa, “Muna maka godiya ya Ubangiji Allah, Maɗaukaki, wanda yake a yanzu, shi ne kuma a dā, domin ka karɓi ikonka mai girma ka kuma fara mulki.
Řkouce: Díky činíme tobě, Pane Bože všemohoucí, Kterýž jsi, a Kterýžs byl, a Kterýž přijíti máš; nebo jsi přijal moc svou velikou a království ujal.
18 Al’ummai suka yi fushi; fushinka kuwa ya zo. Lokaci ya yi don a shari’anta matattu, da kuma don sākawa wa bayinka annabawa da tsarkakanka da kuma su waɗanda suke girmama sunanka, ƙarami da babba, don kuma hallakar da waɗanda suka hallaka duniya.”
I rozhněvali se národové, a přišel hněv tvůj, a čas mrtvých, aby souzeni byli, a aby dána byla odplata služebníkům tvým prorokům, i jiným svatým i všechněm, jenž se bojí jména tvého, malým i velikým, a aby zkaženi byli ti, kteříž nakažují zemi.
19 Sa’an nan aka buɗe haikalin Allah da yake a sama, kuma a cikin haikalinsa aka ga akwatin alkawarinsa. Sai kuwa ga walƙiya, ƙararraki, tsawa, girgizar ƙasa, da kuma ƙanƙara masu girma.
I otevřín jest chrám Boží na nebi, a vidína jest truhla smlouvy jeho v chrámě jeho. I stalo se blýskání, a hlasové, a hromobití, a země třesení, i krupobití veliké.

< Ru’uya ta Yohanna 11 >