< Ru’uya ta Yohanna 10 >

1 Sai na ga wani babban mala’ika yana saukowa daga sama. An lulluɓe shi da girgije, bakan gizo kuma yana kansa; fuskarsa tana kama da rana, ƙafafunsa kuma suna kama da ginshiƙan wuta.
اَنَنْتَرَں سْوَرْگادْ اَوَروہَنْ اَپَرَ ایکو مَہابَلو دُوتو مَیا درِشْٹَح، سَ پَرِہِتَمیگھَسْتَسْیَ شِرَشْچَ میگھَدھَنُشا بھُوشِتَں مُکھَمَنْڈَلَنْچَ سُورْیَّتُلْیَں چَرَنَو چَ وَہْنِسْتَمْبھَسَمَو۔
2 Yana riƙe da ɗan ƙaramin naɗaɗɗen littafi, wanda yake a buɗe a hannunsa. Ya kafa ƙafarsa ta dama a kan teku ƙafarsa ta hagu kuma a kan ƙasa,
سَ سْوَکَرینَ وِسْتِیرْنَمیکَں کْشُودْرَگْرَنْتھَں دھارَیَتِ، دَکْشِنَچَرَنینَ سَمُدْرے وامَچَرَنینَ چَ سْتھَلے تِشْٹھَتِ۔
3 ya kuma yi ihu da ƙarfi kamar rurin zaki. Da ya yi ihun, sai muryoyin tsawan nan bakwai suka yi magana.
سَ سِںہَگَرْجَنَوَدْ اُچَّیحسْوَرینَ نْیَنَدَتْ نِنادے کرِتے سَپْتَ سْتَنِتانِ سْوَکِییانْ سْوَنانْ پْراکاشَیَنْ۔
4 Sa’ad da tsawan nan bakwai kuwa suka yi magana, ina dab da rubutawa; amma na ji wata murya daga sama ta ce, “Rufe abin da tsawan nan bakwai suka faɗa kada ka rubuta.”
تَیح سَپْتَ سْتَنِتَے رْواکْیے کَتھِتے ہَں تَتْ لیکھِتُمْ اُدْیَتَ آسَں کِنْتُ سْوَرْگادْ واگِیَں مَیا شْرُتا سَپْتَ سْتَنِتَے رْیَدْ یَدْ اُکْتَں تَتْ مُدْرَیانْکَیَ ما لِکھَ۔
5 Sai mala’ikan da na gani na tsaye a teku da ƙasa ya ɗaga hannunsa na dama sama.
اَپَرَں سَمُدْرَمیدِنْیوسْتِشْٹھَنْ یو دُوتو مَیا درِشْٹَح سَ گَگَنَں پْرَتِ سْوَدَکْشِنَکَرَمُتّھاپْیَ
6 Ya kuma yi rantsuwa da wannan wanda yake raye har abada abadin, wanda ya halicci sammai da dukan abin da yake cikinsu, duniya da dukan abin da yake cikinta, da kuma teku da dukan abin da yake cikinsa, ya kuma ce, “Babu sauran jinkiri! (aiōn g165)
اَپَرَں سْوَرْگادْ یَسْیَ رَوو مَیاشْراوِ سَ پُنَ رْماں سَمْبھاوْیاوَدَتْ تْوَں گَتْوا سَمُدْرَمیدِنْیوسْتِشْٹھَتو دُوتَسْیَ کَراتْ تَں وِسْتِیرْنَ کْشُدْرَگْرَنْتھَں گرِہانَ، تینَ مَیا دُوتَسَمِیپَں گَتْوا کَتھِتَں گْرَنْتھو سَو دِییَتاں۔ (aiōn g165)
7 Amma a ranakun da mala’ika na bakwai na dab da busa ƙahonsa, za a cika asirin Allah, kamar yadda ya sanar wa bayinsa annabawa.”
کِنْتُ تُورِیں وادِشْیَتَح سَپْتَمَدُوتَسْیَ تُورِیوادَنَسَمَیَ اِیشْوَرَسْیَ گُپْتا مَنْتْرَنا تَسْیَ داسانْ بھَوِشْیَدْوادِنَح پْرَتِ تینَ سُسَںوادے یَتھا پْرَکاشِتا تَتھَیوَ سِدّھا بھَوِشْیَتِ۔
8 Sai muryar da na ji daga sama ta sāke magana da ni ta ce, “Tafi, ka karɓi naɗaɗɗen littafin da yake a buɗe a hannun mala’ikan da yake tsaye bisa teku da ƙasa.”
اَپَرَں سْوَرْگادْ یَسْیَ رَوو مَیاشْراوِ سَ پُنَ رْماں سَمْبھاشْیاوَدَتْ تْوَں گَتْوا سَمُدْرَمیدِنْیوسْتِشْٹھَتو دُوتَسْیَ کَراتْ تَں وِسْتِیرْنَں کْشُدْرَگْرَنْتھَں گرِہانَ،
9 Sai na je wajen mala’ikan na ce masa yă ba ni ƙaramin naɗaɗɗen littafin. Ya ce mini, “Karɓa ka ci. Zai sa cikinka yă yi tsami, amma ‘a bakinka zai zama da zaƙi kamar zuma.’”
تینَ مَیا دُوتَسَمِیپَں گَتْوا کَتھِتَں گْرَنْتھو سَو دِییَتاں۔ سَ مامْ اَوَدَتْ تَں گرِہِیتْوا گِلَ، تَوودَرے سَ تِکْتَرَسو بھَوِشْیَتِ کِنْتُ مُکھے مَدھُوَتْ سْوادُ رْبھَوِشْیَتِ۔
10 Na karɓi ƙaramin naɗaɗɗen littafin daga hannun mala’ikan na kuma ci. Ya yi zaƙi kamar zuma a bakina, amma sa’ad da na cinye, cikina ya yi tsami.
تینَ مَیا دُوتَسْیَ کَرادْ گْرَنْتھو گرِہِیتو گِلِتَشْچَ۔ سَ تُ مَمَ مُکھے مَدھُوَتْ سْوادُراسِیتْ کِنْتْوَدَناتْ پَرَں مَمودَرَسْتِکْتَتاں گَتَح۔
11 Sa’an nan aka ce mini, “Dole ne ka sāke yin annabci game da mutane masu yawa, al’ummai, harsuna da kuma sarakuna.”
تَتَح سَ مامْ اَوَدَتْ بَہُونْ جاتِوَںشَبھاشاوَدِراجانْ اَدھِ تْوَیا پُنَ رْبھَوِشْیَدْواکْیَں وَکْتَوْیَں۔

< Ru’uya ta Yohanna 10 >