< Ru’uya ta Yohanna 10 >

1 Sai na ga wani babban mala’ika yana saukowa daga sama. An lulluɓe shi da girgije, bakan gizo kuma yana kansa; fuskarsa tana kama da rana, ƙafafunsa kuma suna kama da ginshiƙan wuta.
Então, vi outro anjo poderoso, descendo do céu, com uma nuvem em volta dele e com um arco-íris sobre a sua cabeça. O seu rosto era como o sol, e seus pés, como colunas de fogo.
2 Yana riƙe da ɗan ƙaramin naɗaɗɗen littafi, wanda yake a buɗe a hannunsa. Ya kafa ƙafarsa ta dama a kan teku ƙafarsa ta hagu kuma a kan ƙasa,
Ele segurava um pequeno livro que já estava aberto. Ele colocou o seu pé direito no mar e o esquerdo na terra.
3 ya kuma yi ihu da ƙarfi kamar rurin zaki. Da ya yi ihun, sai muryoyin tsawan nan bakwai suka yi magana.
Ele deu um grito bem alto como um leão rugindo. Quando ele gritou, os sete trovões responderam.
4 Sa’ad da tsawan nan bakwai kuwa suka yi magana, ina dab da rubutawa; amma na ji wata murya daga sama ta ce, “Rufe abin da tsawan nan bakwai suka faɗa kada ka rubuta.”
Quando os sete trovões falaram, eu estava quase escrevendo o que eles tinham dito quando ouvi uma voz vinda do céu, que me disse: “Mantenha em segredo o que os sete trovões disseram. Não escreva isso.”
5 Sai mala’ikan da na gani na tsaye a teku da ƙasa ya ɗaga hannunsa na dama sama.
O anjo que eu vi em pé sobre o mar e sobre a terra levantou a sua mão direita em direção ao céu.
6 Ya kuma yi rantsuwa da wannan wanda yake raye har abada abadin, wanda ya halicci sammai da dukan abin da yake cikinsu, duniya da dukan abin da yake cikinta, da kuma teku da dukan abin da yake cikinsa, ya kuma ce, “Babu sauran jinkiri! (aiōn g165)
Ele fez um juramento sagrado para aquele que vive para todo o sempre, que criou o céu, a terra, o mar e tudo que há neles. Ele disse: “Não vai demorar mais!” (aiōn g165)
7 Amma a ranakun da mala’ika na bakwai na dab da busa ƙahonsa, za a cika asirin Allah, kamar yadda ya sanar wa bayinsa annabawa.”
Mas, no momento em que o sétimo anjo falar, quando ele tocar a sua trombeta, então, o mistério de Deus se cumprirá, como ele anunciou aos seus servos, os profetas.
8 Sai muryar da na ji daga sama ta sāke magana da ni ta ce, “Tafi, ka karɓi naɗaɗɗen littafin da yake a buɗe a hannun mala’ikan da yake tsaye bisa teku da ƙasa.”
Então, ouvi novamente a voz vinda do céu me dizer: “Vá e pegue o livro que está aberto na mão do anjo que se encontra em pé sobre o mar e sobre a terra.”
9 Sai na je wajen mala’ikan na ce masa yă ba ni ƙaramin naɗaɗɗen littafin. Ya ce mini, “Karɓa ka ci. Zai sa cikinka yă yi tsami, amma ‘a bakinka zai zama da zaƙi kamar zuma.’”
Então, fui até o anjo e lhe pedi o pequeno livro. Ele disse para mim: “Pegue o livro e coma-o! No seu estômago ele ficará amargo, mas terá um gosto doce como o mel em sua boca.”
10 Na karɓi ƙaramin naɗaɗɗen littafin daga hannun mala’ikan na kuma ci. Ya yi zaƙi kamar zuma a bakina, amma sa’ad da na cinye, cikina ya yi tsami.
Eu peguei o pequeno livro das mãos do anjo e o comi. Em minha boca senti um gosto doce como o mel, mas havia uma sensação de amargo em meu estômago.
11 Sa’an nan aka ce mini, “Dole ne ka sāke yin annabci game da mutane masu yawa, al’ummai, harsuna da kuma sarakuna.”
Diseram-me: “Você deve anunciar novamente a mensagem de Deus a muitos povos, muitas nações, línguas e reis.”

< Ru’uya ta Yohanna 10 >