< Ru’uya ta Yohanna 10 >
1 Sai na ga wani babban mala’ika yana saukowa daga sama. An lulluɓe shi da girgije, bakan gizo kuma yana kansa; fuskarsa tana kama da rana, ƙafafunsa kuma suna kama da ginshiƙan wuta.
Kangi namuwene mtumu yungi wa kunani kwa Chapanga mweavi na makakala ihelela kuhuma kunani. Agubikwi lihundi na upinde wa fula pamutu waki. Pamihu paki pavi ngati lilanga na magendelu gaki gavi ngati mapanda ga motu.
2 Yana riƙe da ɗan ƙaramin naɗaɗɗen littafi, wanda yake a buɗe a hannunsa. Ya kafa ƙafarsa ta dama a kan teku ƙafarsa ta hagu kuma a kan ƙasa,
Mumawoko gaki akamwili chitabu chidebe chechigubukuliwi. Avikili chigendelu chaki cha kulyela panani ya nyanja na cha kumangeya panani ya mulima.
3 ya kuma yi ihu da ƙarfi kamar rurin zaki. Da ya yi ihun, sai muryoyin tsawan nan bakwai suka yi magana.
Akukemela kwa lwami luvaha ngati kubuluma kwa lihimba. Peakwesili lwami, mibulumo saba ya mbamba yayangwili kwa chigigi.
4 Sa’ad da tsawan nan bakwai kuwa suka yi magana, ina dab da rubutawa; amma na ji wata murya daga sama ta ce, “Rufe abin da tsawan nan bakwai suka faɗa kada ka rubuta.”
Mibulumo yila saba payayuwaniki, nene naganili kuyandika. Nambu nayuwini lwami kuhuma kunani kwa Chapanga, “Malovi ga mibulumo ya mbamba saba yila ndi mfiyu ukotoka kuyandika!”
5 Sai mala’ikan da na gani na tsaye a teku da ƙasa ya ɗaga hannunsa na dama sama.
Kangi mtumu wa kunani kwa Chapanga yula mwenamuwene ayimili panani ya nyanja na panani ya pandumba, ayinwili chiwoko chaki cha kulyela kuyelekela kunani kwa Chapanga,
6 Ya kuma yi rantsuwa da wannan wanda yake raye har abada abadin, wanda ya halicci sammai da dukan abin da yake cikinsu, duniya da dukan abin da yake cikinta, da kuma teku da dukan abin da yake cikinsa, ya kuma ce, “Babu sauran jinkiri! (aiōn )
akalapa kwa liina la Chapanga mweitama magono goha gangali mwishu, Chapanga mweawumbili kunani na vindu vyoha vyevivii na mweawumbili nyanja vyoha vyevivii na mweawumbili pamulima na vyoha vyevivii. Akajova, “Lukumbi lwa kulindila neju lumaliki! (aiōn )
7 Amma a ranakun da mala’ika na bakwai na dab da busa ƙahonsa, za a cika asirin Allah, kamar yadda ya sanar wa bayinsa annabawa.”
Nambu lukumbi mtumu wa kunani kwa Chapanga wa saba peipyula lipenenga laki, Chapanga yati imakilisila mpangu waki wa mfiyu ngati cheavajovili vatumisi vaki vamlota va Chapanga.”
8 Sai muryar da na ji daga sama ta sāke magana da ni ta ce, “Tafi, ka karɓi naɗaɗɗen littafin da yake a buɗe a hannun mala’ikan da yake tsaye bisa teku da ƙasa.”
Kangi, lwami lula lwenaluyuwini kuhuma kunani kwa Chapanga kadeni, lukajova na nene kavili, “Hamba ukatola chitabu chila chechigubukuliwi, chechivii mu mawoko ga mtumu wa kunani kwa Chapanga mweayimili panani ya nyanja na pandumba.”
9 Sai na je wajen mala’ikan na ce masa yă ba ni ƙaramin naɗaɗɗen littafin. Ya ce mini, “Karɓa ka ci. Zai sa cikinka yă yi tsami, amma ‘a bakinka zai zama da zaƙi kamar zuma.’”
Hinu, namuhambili mtumu wa kunani kwa Chapanga, nikamjovela anipela chitabu chila chidebe. Mwene anijovili, “Tola, ulyayi, mumlomo waku yati chinoga ngati wuchi, nambu mwileme yati chivya chivavanu!”
10 Na karɓi ƙaramin naɗaɗɗen littafin daga hannun mala’ikan na kuma ci. Ya yi zaƙi kamar zuma a bakina, amma sa’ad da na cinye, cikina ya yi tsami.
Ndi nachitolili chitabu chidebe chila kuhuma mu mawoko ga mtumu wa kunani kwa Chapanga. Nalili chene chanogayi mumlomo wangu ngati wuchi, nambu panamilili chang'anamwiki kuvya chivavanu mwileme.
11 Sa’an nan aka ce mini, “Dole ne ka sāke yin annabci game da mutane masu yawa, al’ummai, harsuna da kuma sarakuna.”
Kangi akanijovela, “Yikukugana kujova kavili ujumbi wa Chapanga ndava ya vandu vamahele na milima yamahele na luga zamahele na vankosi!”