< Ru’uya ta Yohanna 10 >
1 Sai na ga wani babban mala’ika yana saukowa daga sama. An lulluɓe shi da girgije, bakan gizo kuma yana kansa; fuskarsa tana kama da rana, ƙafafunsa kuma suna kama da ginshiƙan wuta.
And I saw another mighty angel coming down from heaven invested with a cloud: and there was a rainbow on his head, and his face was as the sun, and his feet as pillars of fire.
2 Yana riƙe da ɗan ƙaramin naɗaɗɗen littafi, wanda yake a buɗe a hannunsa. Ya kafa ƙafarsa ta dama a kan teku ƙafarsa ta hagu kuma a kan ƙasa,
And he had in his hand a little book open: and he set his right foot upon the sea, and his left upon the earth.
3 ya kuma yi ihu da ƙarfi kamar rurin zaki. Da ya yi ihun, sai muryoyin tsawan nan bakwai suka yi magana.
And he cried with a loud voice like the roaring of a lion; and when he had cried, seven thunders uttered their voices.
4 Sa’ad da tsawan nan bakwai kuwa suka yi magana, ina dab da rubutawa; amma na ji wata murya daga sama ta ce, “Rufe abin da tsawan nan bakwai suka faɗa kada ka rubuta.”
And when the seven thunders had uttered their voices, I was going to write: but I heard a voice from heaven saying unto me, Seal up what the seven thunders spake, and write them not.
5 Sai mala’ikan da na gani na tsaye a teku da ƙasa ya ɗaga hannunsa na dama sama.
And the angel which I saw standing on the sea and on the earth,
6 Ya kuma yi rantsuwa da wannan wanda yake raye har abada abadin, wanda ya halicci sammai da dukan abin da yake cikinsu, duniya da dukan abin da yake cikinta, da kuma teku da dukan abin da yake cikinsa, ya kuma ce, “Babu sauran jinkiri! (aiōn )
lifted up his hand to heaven, and sware by Him that liveth for ever, who created the heaven and the things therein, and the earth and the things that are in it, and the sea and the things therein, that there shall be time no longer: (aiōn )
7 Amma a ranakun da mala’ika na bakwai na dab da busa ƙahonsa, za a cika asirin Allah, kamar yadda ya sanar wa bayinsa annabawa.”
but in the days of the voice of the seventh angel, when he shall sound his trumpet, the mystery of God shall be finished, as He hath declared to his servants the prophets.
8 Sai muryar da na ji daga sama ta sāke magana da ni ta ce, “Tafi, ka karɓi naɗaɗɗen littafin da yake a buɗe a hannun mala’ikan da yake tsaye bisa teku da ƙasa.”
And the voice, which I heard from heaven, spake to me again, and said, Go, take the little book which is open in the hand of the angel that standeth upon the sea and upon the earth.
9 Sai na je wajen mala’ikan na ce masa yă ba ni ƙaramin naɗaɗɗen littafin. Ya ce mini, “Karɓa ka ci. Zai sa cikinka yă yi tsami, amma ‘a bakinka zai zama da zaƙi kamar zuma.’”
And I went to the angel, and said to him, Give me the little book. And he said to me, Take it, and eat it up: and it shall make thy belly bitter, but in thy mouth it will be sweet as honey.
10 Na karɓi ƙaramin naɗaɗɗen littafin daga hannun mala’ikan na kuma ci. Ya yi zaƙi kamar zuma a bakina, amma sa’ad da na cinye, cikina ya yi tsami.
And I took the little book out of the angel's hand, and ate it up: and it was in my mouth sweet as honey, and when I had eaten it my belly was bitter.
11 Sa’an nan aka ce mini, “Dole ne ka sāke yin annabci game da mutane masu yawa, al’ummai, harsuna da kuma sarakuna.”
And he said unto me, Thou must prophesy again of many people and nations and tongues and kings.