< Ru’uya ta Yohanna 1 >

1 Wahayin Yesu Kiristi, wanda Allah ya ba shi yă nuna wa bayinsa abin da lalle zai faru nan ba da daɗewa ba. Ya bayyana shi ta wurin aiko da mala’ikansa zuwa ga bawansa Yohanna,
یَتْ پْرَکاشِتَں واکْیَمْ اِیشْوَرَح سْوَداساناں نِکَٹَں شِیگھْرَمُپَسْتھاسْیَنْتِیناں گھَٹَناناں دَرْشَنارْتھَں یِیشُکھْرِیشْٹے سَمَرْپِتَوانْ تَتْ سَ سْوِییَدُوتَں پْریشْیَ نِجَسیوَکَں یوہَنَں جْناپِتَوانْ۔
2 wanda ya shaida dukan abin da ya gani, wato, maganar Allah da kuma shaidar Yesu Kiristi.
سَ چیشْوَرَسْیَ واکْیے کھْرِیشْٹَسْیَ ساکْشْیے چَ یَدْیَدْ درِشْٹَوانْ تَسْیَ پْرَمانَں دَتَّوانْ۔
3 Mai albarka ne wanda yake karanta waɗannan kalmomin annabci, masu albarka ne kuma waɗanda suke jinsu, suke kuma sa abin da aka rubuta a ciki a zuciya, domin lokaci ya yi kusa.
ایتَسْیَ بھَوِشْیَدْوَکْترِگْرَنْتھَسْیَ واکْیاناں پاٹھَکَح شْروتارَشْچَ تَنْمَدھْیے لِکھِتاجْناگْراہِنَشْچَ دھَنْیا یَتَح سَ کالَح سَنِّکَٹَح۔
4 Daga Yohanna, Zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai da suke a lardin Asiya. Alheri da salama gare ku daga shi wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, da kuma daga ruhohi bakwai da suke a gaban kursiyinsa,
یوہَنْ آشِیادیشَسْتھاح سَپْتَ سَمِتِیح پْرَتِ پَتْرَں لِکھَتِ۔ یو وَرْتَّمانو بھُوتو بھَوِشْیَںشْچَ یے چَ سَپْتاتْمانَسْتَسْیَ سِںہاسَنَسْیَ سَمُّکھے تِشْٹھَنْتِ
5 da kuma daga Yesu Kiristi, wanda yake amintaccen shaida, ɗan farin daga tashin matattu, da kuma mai mulkin sarakunan duniya. Gare shi wanda yake ƙaunarmu wanda kuma ya’yantar da mu daga zunubanmu ta wurin jininsa,
یَشْچَ یِیشُکھْرِیشْٹو وِشْوَسْتَح ساکْشِی مرِتاناں مَدھْیے پْرَتھَمَجاتو بھُومَنْڈَلَسْتھَراجانامْ اَدھِپَتِشْچَ بھَوَتِ، ایتیبھْیو نُگْرَہَح شانْتِشْچَ یُشْماسُ وَرْتَّتاں۔
6 ya kuma mai da mu masarauta da firistoci don mu yi wa Allahnsa da Ubansa hidima, a gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin! Amin. (aiōn g165)
یو سْماسُ پْرِیتَوانْ سْوَرُدھِریناسْمانْ سْوَپاپیبھْیَح پْرَکْشالِتَوانْ تَسْیَ پِتُرِیشْوَرَسْیَ یاجَکانْ کرِتْواسْمانْ راجَوَرْگے نِیُکْتَواںشْچَ تَسْمِنْ مَہِما پَراکْرَمَشْچانَنْتَکالَں یاوَدْ وَرْتَّتاں۔ آمینْ۔ (aiōn g165)
7 “Duba, yana zuwa cikin gizagizai, kowane ido kuwa zai gan shi, har da waɗanda suka soke shi”; dukan mutanen duniya kuwa “za su yi makoki dominsa.”
پَشْیَتَ سَ میگھَیراگَچّھَتِ تینَیکَیکَسْیَ چَکْشُسْتَں دْرَکْشْیَتِ یے چَ تَں وِدّھَوَنْتَسْتے پِ تَں وِلوکِشْیَنْتے تَسْیَ کرِتے پرِتھِوِیسْتھاح سَرْوّے وَںشا وِلَپِشْیَنْتِ۔ سَتْیَمْ آمینْ۔
8 “Ni ne Alfa da kuma Omega,” in ji Ubangiji Allah, “wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, Maɗaukaki.”
وَرْتَّمانو بھُوتو بھَوِشْیَںشْچَ یَح سَرْوَّشَکْتِمانْ پْرَبھُح پَرَمیشْوَرَح سَ گَدَتِ، اَہَمیوَ کَح کْشَشْچارْتھَتَ آدِرَنْتَشْچَ۔
9 Ni, Yohanna, ɗan’uwanku da kuma abokin tarayyarku cikin wahala da mulki, da kuma haƙurin jimrewa da suke namu cikin Yesu, ina can tsibirin Fatmos saboda maganar Allah da kuma saboda shaidar Yesu.
یُشْماکَں بھْراتا یِیشُکھْرِیشْٹَسْیَ کْلیشَراجْیَتِتِکْشاناں سَہَبھاگِی چاہَں یوہَنْ اِیشْوَرَسْیَ واکْیَہیتو رْیِیشُکھْرِیشْٹَسْیَ ساکْشْیَہیتوشْچَ پاتْمَنامَکَ اُپَدْوِیپَ آسَں۔
10 A Ranar Ubangiji ina cikin Ruhu, sai na ji a bayana wata babbar murya kamar ƙaho,
تَتْرَ پْرَبھو رْدِنے آتْمَناوِشْٹو ہَں سْوَپَشْچاتْ تُورِیدھْوَنِوَتْ مَہارَوَمْ اَشْرَوشَں،
11 wadda ta ce, “Rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi abin da ka gani ka kuma aika ta zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai, zuwa Afisa, Simirna, Fergamum, Tiyatira, Sardis, Filadelfiya, da kuma Lawodiseya.”
تینوکْتَمْ، اَہَں کَح کْشَشْچارْتھَتَ آدِرَنْتَشْچَ۔ تْوَں یَدْ دْرَکْشْیَسِ تَدْ گْرَنْتھے لِکھِتْواشِیادیشَسْتھاناں سَپْتَ سَمِتِیناں سَمِیپَمْ اِپھِشَں سْمُرْناں تھُیاتِیراں سارْدِّں پھِلادِلْپھِیاں لایَدِیکییانْچَ پْریشَیَ۔
12 Sai na juya don in ga muryar da take magana da ni. Da na juya kuwa sai na ga alkukan fitilu bakwai na zinariya.
تَتو مَیا سَمْبھاشَمانَسْیَ کَسْیَ رَوَح شْرُویَتے تَدَّرْشَنارْتھَں مُکھَں پَراوَرْتِّتَں تَتْ پَراوَرْتْیَ سْوَرْنَمَیاح سَپْتَ دِیپَورِکْشا درِشْٹاح۔
13 A tsakiyar alkukan kuwa akwai wani “kama da ɗan mutum,” saye da rigar da ya kai har ƙafafunsa da kuma ɗamarar zinariya daure a ƙirjinsa.
تیشاں سَپْتَ دِیپَورِکْشاناں مَدھْیے دِیرْگھَپَرِچّھَدَپَرِہِتَح سُوَرْنَشرِنْکھَلینَ ویشْٹِتَوَکْشَشْچَ مَنُشْیَپُتْراکرِتِریکو جَنَسْتِشْٹھَتِ،
14 Kansa da kuma gashin fari ne fat kamar ulu, fari kamar dusar ƙanƙara, idanunsa kuwa kamar harshen wuta.
تَسْیَ شِرَح کیشَشْچَ شْویتَمیشَلومانِیوَ ہِمَوَتْ شْریتَو لوچَنے وَہْنِشِکھاسَمی
15 Sawunsa sun yi kamar tagullar da take haske cikin matoya, muryarsa kuma ta yi kamar muryar ruwaye masu gudu.
چَرَنَو وَہْنِکُنْڈیتاپِتَسُپِتَّلَسَدرِشَو رَوَشْچَ بَہُتویاناں رَوَتُلْیَح۔
16 A hannunsa na dama ya riƙe taurari bakwai, daga bakinsa kuwa takobi mai kaifi biyu ya fito. Fuskarsa ta yi kamar rana mai haskakawa da dukan haskenta.
تَسْیَ دَکْشِنَہَسْتے سَپْتَ تارا وِدْیَنْتے وَکْتْراچَّ تِیکْشْنو دْوِدھارَح کھَنْگو نِرْگَچّھَتِ مُکھَمَنْڈَلَنْچَ سْوَتیجَسا دیدِیپْیَمانَسْیَ سُورْیَّسْیَ سَدرِشَں۔
17 Sa’ad da na gan shi, sai na fāɗi a gabansa sai ka ce matacce. Sai ya ɗibiya hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Ni ne Farko da kuma Ƙarshe.
تَں درِشْٹْواہَں مرِتَکَلْپَسْتَچَّرَنے پَتِتَسْتَتَح سْوَدَکْشِنَکَرَں مَیِ نِدھایَ تینوکْتَمْ ما بھَیشِیح؛ اَہَمْ آدِرَنْتَشْچَ۔
18 Ni ne Rayayye, dā na mutu, ga shi kuwa ina a raye har abada abadin! Ina kuma riƙe da mabuɗan mutuwa da na Hades. (aiōn g165, Hadēs g86)
اَہَمْ اَمَرَسْتَتھاپِ مرِتَوانْ کِنْتُ پَشْیاہَمْ اَنَنْتَکالَں یاوَتْ جِیوامِ۔ آمینْ۔ مرِتْیوح پَرَلوکَسْیَ چَ کُنْجِکا مَمَ ہَسْتَگَتاح۔ (aiōn g165, Hadēs g86)
19 “Saboda haka, ka rubuta abin da ka gani, abin da yake yanzu, da abin da zai faru nan gaba.
اَتو یَدْ بھَوَتِ یَچّیتَح پَرَں بھَوِشْیَتِ تْوَیا درِشْٹَں تَتْ سَرْوَّں لِکھْیَتاں۔
20 Asirin taurari bakwai da ka gani a hannuna na dama da kuma na alkukan fitilu bakwai na zinariya shi ne, Taurarin bakwai ɗin nan, mala’ikun ikkilisiyoyi bakwai ne; alkukan fitilu bakwai ɗin nan kuma ikkilisiyoyi bakwai ne.
مَمَ دَکْشِنَہَسْتے سْتھِتا یاح سَپْتَ تارا یے چَ سْوَرْنَمَیاح سَپْتَ دِیپَورِکْشاسْتْوَیا درِشْٹاسْتَتّاتْپَرْیَّمِدَں تاح سَپْتَ تاراح سَپْتَ سَمِتِیناں دُوتاح سُوَرْنَمَیاح سَپْتَ دِیپَورِکْشاشْچَ سَپْتَ سَمِتَیَح سَنْتِ۔

< Ru’uya ta Yohanna 1 >