< Ru’uya ta Yohanna 1 >

1 Wahayin Yesu Kiristi, wanda Allah ya ba shi yă nuna wa bayinsa abin da lalle zai faru nan ba da daɗewa ba. Ya bayyana shi ta wurin aiko da mala’ikansa zuwa ga bawansa Yohanna,
این است مکاشفۀ عیسی مسیح که خدا به او داد تا آنچه را که می‌بایست به زودی واقع شود، به خادمانش نشان دهد. او فرشتۀ خود را فرستاد تا این مکاشفه را بر خادم خود یوحنا آشکار سازد.
2 wanda ya shaida dukan abin da ya gani, wato, maganar Allah da kuma shaidar Yesu Kiristi.
یوحنا نیز تمام سخنان خدا و عیسی مسیح و هر آنچه را که خود دید و شنید، به نگارش درآورد.
3 Mai albarka ne wanda yake karanta waɗannan kalmomin annabci, masu albarka ne kuma waɗanda suke jinsu, suke kuma sa abin da aka rubuta a ciki a zuciya, domin lokaci ya yi kusa.
خوشا به حال کسی که این کلام نبوّت را می‌خواند و خوشا به حال آنان که به آن گوش فرا می‌دهند، و آنچه را در آن نوشته شده، نگاه می‌دارند، زیرا زمان وقوع این رویدادها نزدیک است.
4 Daga Yohanna, Zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai da suke a lardin Asiya. Alheri da salama gare ku daga shi wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, da kuma daga ruhohi bakwai da suke a gaban kursiyinsa,
از طرف یوحنا، به هفت کلیسا که در ایالت آسیا هستند. فیض و آرامش بر شما باد، از جانب پروردگاری که هست و بود و می‌آید، و از جانب روح هفتگانه که در پیشگاه تخت الهی است،
5 da kuma daga Yesu Kiristi, wanda yake amintaccen shaida, ɗan farin daga tashin matattu, da kuma mai mulkin sarakunan duniya. Gare shi wanda yake ƙaunarmu wanda kuma ya’yantar da mu daga zunubanmu ta wurin jininsa,
و از جانب عیسی مسیح که تمام حقیقت را به طور کامل بر ما آشکار می‌فرماید. مسیح نخستین کسی است که پس از مرگ زنده شد، و برتر از تمام پادشاهان این جهان است. سپاس و ستایش بر او که ما را محبت می‌نماید و با خون خود ما را شست و از گناهانمان رهانید؛
6 ya kuma mai da mu masarauta da firistoci don mu yi wa Allahnsa da Ubansa hidima, a gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin! Amin. (aiōn g165)
او ما را در پادشاهی خود، کاهنان منصوب کرده تا خدا یعنی پدر او را خدمت نماییم. او را تا ابد قدرت و جلال باد! آمین. (aiōn g165)
7 “Duba, yana zuwa cikin gizagizai, kowane ido kuwa zai gan shi, har da waɗanda suka soke shi”; dukan mutanen duniya kuwa “za su yi makoki dominsa.”
بنگرید! او سوار بر ابرها می‌آید. هر چشمی او را خواهد دید؛ حتی آنانی که به او نیزه زدند، او را خواهند دید؛ و تمام قومهای جهان برای او سوگواری خواهند کرد. بله، آمین! بگذار چنین باشد.
8 “Ni ne Alfa da kuma Omega,” in ji Ubangiji Allah, “wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, Maɗaukaki.”
خدا می‌فرماید: «من الف و یا هستم. من ابتدا و انتها هستم.» این را خداوندی می‌فرماید که صاحب تمام قدرتهاست، و هست و بود و می‌آید.
9 Ni, Yohanna, ɗan’uwanku da kuma abokin tarayyarku cikin wahala da mulki, da kuma haƙurin jimrewa da suke namu cikin Yesu, ina can tsibirin Fatmos saboda maganar Allah da kuma saboda shaidar Yesu.
من، یوحنا، که این نامه را برای شما می‌نویسم، مانند شما در راه خداوند رنج می‌کشم. اما او به ما صبر و تحمل عطا فرموده و ما را در ملکوت خود سهیم نموده است. من به علّت اعلام پیغام انجیل و بشارت دربارهٔ عیسی، به جزیرهٔ پطموس تبعید شدم.
10 A Ranar Ubangiji ina cikin Ruhu, sai na ji a bayana wata babbar murya kamar ƙaho,
در روزِ خداوند، روح خدا مرا فرو گرفت. ناگهان از پشت سر خود، صدایی بلند همچون صدای شیپور شنیدم،
11 wadda ta ce, “Rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi abin da ka gani ka kuma aika ta zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai, zuwa Afisa, Simirna, Fergamum, Tiyatira, Sardis, Filadelfiya, da kuma Lawodiseya.”
که می‌گفت: «من الف و یا هستم. من ابتدا و انتها هستم. هر چه می‌بینی، در نامه‌ای بنویس و آن را برای هفت کلیسا بفرست، یعنی برای کلیساهای اَفِسُس، اِسمیرنا، پِرگاموم، تیاتیرا، ساردِس، فیلادِلفیه و لائودیکیه.»
12 Sai na juya don in ga muryar da take magana da ni. Da na juya kuwa sai na ga alkukan fitilu bakwai na zinariya.
هنگامی که برگشتم تا کسی را که با من سخن می‌گفت ببینم، در پشت سر خود هفت شمعدان طلا دیدم.
13 A tsakiyar alkukan kuwa akwai wani “kama da ɗan mutum,” saye da rigar da ya kai har ƙafafunsa da kuma ɗamarar zinariya daure a ƙirjinsa.
در میان شمعدانها، مردی را دیدم شبیه پسر انسان که ردایی بلند بر تن داشت و کمربندی طلایی دور سینه‌اش بود.
14 Kansa da kuma gashin fari ne fat kamar ulu, fari kamar dusar ƙanƙara, idanunsa kuwa kamar harshen wuta.
سر و موی او سفید بود چون برف و پشم، و چشمانش تیز و نافذ بود همچون شعله‌های آتش.
15 Sawunsa sun yi kamar tagullar da take haske cikin matoya, muryarsa kuma ta yi kamar muryar ruwaye masu gudu.
پاهای او می‌درخشید، مانند مسی که در کورۀ آتش صیقل داده باشند. صدای او مثل آبشار طنین‌افکن بود.
16 A hannunsa na dama ya riƙe taurari bakwai, daga bakinsa kuwa takobi mai kaifi biyu ya fito. Fuskarsa ta yi kamar rana mai haskakawa da dukan haskenta.
در دست راست او، هفت ستاره بود، و شمشیر دو دمِ تیزی هم در دهانش قرار داشت. صورت او همچون خورشید بود در درخشش کاملش.
17 Sa’ad da na gan shi, sai na fāɗi a gabansa sai ka ce matacce. Sai ya ɗibiya hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Ni ne Farko da kuma Ƙarshe.
وقتی چشمم به او افتاد، مانند مرده جلوی پای او افتادم. اما او دست راست خود را بر من گذاشت و فرمود: «نترس! من ابتدا و انتها هستم! من زنده بودم و مُردم، و حال تا به ابد زنده‌ام، و کلیدهای مرگ و عالم مردگان را در دست دارم. (aiōn g165, Hadēs g86)
18 Ni ne Rayayye, dā na mutu, ga shi kuwa ina a raye har abada abadin! Ina kuma riƙe da mabuɗan mutuwa da na Hades. (aiōn g165, Hadēs g86)
19 “Saboda haka, ka rubuta abin da ka gani, abin da yake yanzu, da abin da zai faru nan gaba.
«پس آنچه دیده‌ای، یعنی آنچه الان در حال وقوع است و آنچه از این پس خواهد شد، همه را بنویس.
20 Asirin taurari bakwai da ka gani a hannuna na dama da kuma na alkukan fitilu bakwai na zinariya shi ne, Taurarin bakwai ɗin nan, mala’ikun ikkilisiyoyi bakwai ne; alkukan fitilu bakwai ɗin nan kuma ikkilisiyoyi bakwai ne.
معنی هفت ستاره‌ای که در دست راست من دیدی و همچنین هفت شمعدان طلا این است: هفت ستاره، فرشتگان هفت کلیسا هستند، و هفت شمعدان، خود هفت کلیسا می‌باشند.

< Ru’uya ta Yohanna 1 >