< Ru’uya ta Yohanna 1 >
1 Wahayin Yesu Kiristi, wanda Allah ya ba shi yă nuna wa bayinsa abin da lalle zai faru nan ba da daɗewa ba. Ya bayyana shi ta wurin aiko da mala’ikansa zuwa ga bawansa Yohanna,
Jesu Kristi Åbenbaring, som Gud gav ham for at vise sine Tjenere, hvad der skal ske snart, og han sendte Bud ved sin Engel og fremstillede det i Billeder for sin Tjener Johannes,
2 wanda ya shaida dukan abin da ya gani, wato, maganar Allah da kuma shaidar Yesu Kiristi.
som har vidnet om Guds Ord og Jesu Kristi Vidnesbyrd: Alt, hvad han har set.
3 Mai albarka ne wanda yake karanta waɗannan kalmomin annabci, masu albarka ne kuma waɗanda suke jinsu, suke kuma sa abin da aka rubuta a ciki a zuciya, domin lokaci ya yi kusa.
Salig er den, som oplæser, og de, som høre Profetiens Ord og bevare det, som er skrevet i den; thi Tiden er nær.
4 Daga Yohanna, Zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai da suke a lardin Asiya. Alheri da salama gare ku daga shi wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, da kuma daga ruhohi bakwai da suke a gaban kursiyinsa,
Johannes til de syv Menigheder i Asien: Nåde være med eder og Fred fra ham, som er, og som var, og som kommer, og fra de syv Ånder, som ere foran hans Trone,
5 da kuma daga Yesu Kiristi, wanda yake amintaccen shaida, ɗan farin daga tashin matattu, da kuma mai mulkin sarakunan duniya. Gare shi wanda yake ƙaunarmu wanda kuma ya’yantar da mu daga zunubanmu ta wurin jininsa,
og fra Jesus Kristus, det troværdige Vidne, den førstefødte af de døde og Jordens Kongers Fyrste. Ham, som elsker os og har udløst os af vore Synder med sit Blod
6 ya kuma mai da mu masarauta da firistoci don mu yi wa Allahnsa da Ubansa hidima, a gare shi ɗaukaka da iko sun tabbata har abada abadin! Amin. (aiōn )
og har gjort os til et Kongerige, til Præster for sin Gud og Fader: Ham være Æren og Magten i Evighedernes Evigheder! Amen. (aiōn )
7 “Duba, yana zuwa cikin gizagizai, kowane ido kuwa zai gan shi, har da waɗanda suka soke shi”; dukan mutanen duniya kuwa “za su yi makoki dominsa.”
Se, han kommer med Skyerne, og hvert Øje skal se ham, også de, som have gennemstunget ham, og alle Jordens Stammer skulle jamre ved hans Komme. Ja, Amen!
8 “Ni ne Alfa da kuma Omega,” in ji Ubangiji Allah, “wanda yake a yanzu, wanda yake a dā, da kuma wanda zai zo, Maɗaukaki.”
Jeg er Alfa og Omega, siger Gud Herren, han, som er, og som var, og som kommer, den Almægtige.
9 Ni, Yohanna, ɗan’uwanku da kuma abokin tarayyarku cikin wahala da mulki, da kuma haƙurin jimrewa da suke namu cikin Yesu, ina can tsibirin Fatmos saboda maganar Allah da kuma saboda shaidar Yesu.
Jeg Johannes, eders Broder og meddelagtig i Trængselen og Riget og Udholdenheden i Jesus, var på den Ø, som kaldes Patmos, for Guds Ords og for Jesu Vidnesbyrds Skyld.
10 A Ranar Ubangiji ina cikin Ruhu, sai na ji a bayana wata babbar murya kamar ƙaho,
Jeg henryktes i Ånden på Herrens Dag, og jeg hørte bag mig en høj Røst som af en Basun, der sagde:
11 wadda ta ce, “Rubuta a cikin naɗaɗɗen littafi abin da ka gani ka kuma aika ta zuwa ga ikkilisiyoyi bakwai, zuwa Afisa, Simirna, Fergamum, Tiyatira, Sardis, Filadelfiya, da kuma Lawodiseya.”
Hvad du ser, skriv det i en Bog, og send det til de syv Menigheder, til Efesus og til Smyrna og til Pergamus og til Thyatira og til Sardes og til Filidelfia og til Laodikea.
12 Sai na juya don in ga muryar da take magana da ni. Da na juya kuwa sai na ga alkukan fitilu bakwai na zinariya.
Og jeg vendte mig for at se Røsten, som talte med mig; og da jeg vendte mig, så jeg syv Guldlysestager
13 A tsakiyar alkukan kuwa akwai wani “kama da ɗan mutum,” saye da rigar da ya kai har ƙafafunsa da kuma ɗamarar zinariya daure a ƙirjinsa.
og midt imellem de syv Lysestager en, lig en Menneskesøn, iført en fodsid Kjortel og omgjordet om Brystet med et Guldbælte.
14 Kansa da kuma gashin fari ne fat kamar ulu, fari kamar dusar ƙanƙara, idanunsa kuwa kamar harshen wuta.
Men hans Hoved og Hår var hvidt som hvid Uld, som Sne; og hans Øjne som Ildslue;
15 Sawunsa sun yi kamar tagullar da take haske cikin matoya, muryarsa kuma ta yi kamar muryar ruwaye masu gudu.
og hans Fødder lignede skinnende Malm, når det gløder i Ovnen; og hans Røst var som mange Vandes Lyd;
16 A hannunsa na dama ya riƙe taurari bakwai, daga bakinsa kuwa takobi mai kaifi biyu ya fito. Fuskarsa ta yi kamar rana mai haskakawa da dukan haskenta.
og i sin højre Hånd havde han syv Stjerner; og af hans Mund udgik der et tveægget, skarpt Sværd, og hans Udseende var som Solen, når den skinner i sin Kraft.
17 Sa’ad da na gan shi, sai na fāɗi a gabansa sai ka ce matacce. Sai ya ɗibiya hannunsa na dama a kaina ya ce, “Kada ka ji tsoro. Ni ne Farko da kuma Ƙarshe.
Og da jeg så ham, faldt jeg ned for hans Fødder som død; og han lagde sin højre Hånd på mig og sagde:
18 Ni ne Rayayye, dā na mutu, ga shi kuwa ina a raye har abada abadin! Ina kuma riƙe da mabuɗan mutuwa da na Hades. (aiōn , Hadēs )
Frygt ikke! Jeg er den første og den sidste og den levende; og jeg var død, og se, jeg er levende i Evighedernes Evigheder, og jeg har Dødens og Dødsrigets Nøgler. (aiōn , Hadēs )
19 “Saboda haka, ka rubuta abin da ka gani, abin da yake yanzu, da abin da zai faru nan gaba.
Skriv derfor, hvad du så, både det, som er, og det, som skal ske herefter.
20 Asirin taurari bakwai da ka gani a hannuna na dama da kuma na alkukan fitilu bakwai na zinariya shi ne, Taurarin bakwai ɗin nan, mala’ikun ikkilisiyoyi bakwai ne; alkukan fitilu bakwai ɗin nan kuma ikkilisiyoyi bakwai ne.
Dette er de syv Stjerners Hemmelighed, hvilke du har set i min højre Hånd, og de syv Guldlysestager: de syv Stjerner ere de syv Menigheders Engle, og de syv Lysestager ere syv Menigheder.