< Zabura 1 >

1 Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
Ne mutlu o insana ki, kötülerin öğüdüyle yürümez, Günahkârların yolunda durmaz, Alaycıların arasında oturmaz.
2 Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
Ancak zevkini RAB'bin Yasası'ndan alır Ve gece gündüz onun üzerinde derin derin düşünür.
3 Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
Böylesi akarsu kıyılarına dikilmiş ağaca benzer, Meyvesini mevsiminde verir, Yaprağı hiç solmaz. Yaptığı her işi başarır.
4 Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
Kötüler böyle değil, Rüzgarın savurduğu saman çöpüne benzerler.
5 Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
Bu yüzden yargılanınca aklanamaz, Doğrular topluluğunda yer bulamaz günahkârlar.
6 Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.
Çünkü RAB doğruların yolunu gözetir, Kötülerin yolu ise ölüme götürür.

< Zabura 1 >