< Zabura 1 >

1 Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
Blessed is the one who doesn't follow the advice of the wicked, or take the path of sinners, or join in with scoffers.
2 Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
But his delight is in the law of the LORD, and on his law he meditates day and night.
3 Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
He will be like a tree planted by the streams of water, that brings forth its fruit in its season, whose leaf also does not wither, and whatever he does shall prosper.
4 Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
Not so with the wicked; instead, they are like the chaff which the wind drives away.
5 Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
Therefore the wicked shall not stand in the judgment, nor sinners in the congregation of the righteous.
6 Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.
For the LORD knows the way of the righteous, but the way of the wicked shall perish.

< Zabura 1 >