< Zabura 99 >
1 Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
RAB egemenlik sürüyor, titresin halklar! Keruvlar arasında tahtına oturmuş, Sarsılsın yeryüzü!
2 Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
RAB Siyon'da uludur, Yücedir O, bütün halklara egemendir.
3 Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
Övsünler büyük, müthiş adını! O kutsaldır.
4 Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
Ey adaleti seven güçlü kral, Eşitliği sen sağladın, Yakup soyunda doğru ve adil olanı sen yaptın.
5 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
Yüceltin Tanrımız RAB'bi, Ayaklarının taburesi önünde tapının! O kutsaldır.
6 Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
Musa'yla Harun O'nun kâhinlerindendi, Samuel de O'nu adıyla çağıranlar arasındaydı. RAB'be seslenirlerdi, O da yanıtlardı.
7 Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
Bulut sütunu içinden onlarla konuştu, Uydular O'nun buyruklarına, Kendilerine verdiği kurallara.
8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
Ya RAB Tanrımız, yanıt verdin onlara; Bağışlayıcı bir Tanrı oldun, Ama yaptıkları kötülüğü cezasız bırakmadın.
9 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.
Tanrımız RAB'bi yüceltin, Tapının O'na kutsal dağında! Çünkü Tanrımız RAB kutsaldır.