< Zabura 99 >
1 Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
¡Yavé reina! ¡Tiemblen los pueblos! Él mora entre los querubines. ¡Que se conmueva la tierra!
2 Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
Yavé es grande en Sion, Y Él es exaltado sobre todos los pueblos.
3 Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
Que alaben tu grande y asombroso Nombre. ¡Santo es Él!
4 Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
La fuerza del Rey ama la justicia. Tú has ejecutado equidad y justicia en Jacob.
5 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
Exalten a Yavé nuestro ʼElohim, Y póstrense ante el estrado de sus pies, ¡Santo es Él!
6 Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
Moisés y Aarón estuvieron entre sus sacerdotes, Y Samuel estuvo entre los que invocaron su Nombre. Invocaban a Yavé, y Él les respondía.
7 Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
En la columna de nube hablaba con ellos. Ellos guardaron sus Testimonios y el estatuto que Él les dio.
8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
Oh Yavé, ʼElohim nuestro, Tú les respondías. Fuiste para ellos un ʼEL perdonador, Aunque vindicador de sus [malas] obras.
9 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.
Exalten a Yavé nuestro ʼElohim Y póstrense hacia su Montaña Santa, Porque Yavé nuestro ʼElohim es santo.