< Zabura 99 >
1 Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
Gospod kraljuje; naj ljudstva trepetajo. On sedi med kerubi; naj bo zemlja omajana.
2 Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
Gospod je velik na Sionu; visoko je nad vsemi ljudstvi.
3 Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
Naj hvalijo tvoje veliko in strašno ime, kajti sveto je.
4 Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
Kraljeva moč ljubi tudi sodbo. Ti utrjuješ nepristranskost, izvršuješ sodbo in pravičnost v Jakobu.
5 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
Povišujte Gospoda, našega Boga in obožujte pri njegovi pručki, kajti on je svet.
6 Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
Mojzes in Aron med njegovimi duhovniki in Samuel med tistimi, ki kličejo njegovo ime; klicali so Gospoda in jim je odgovoril.
7 Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
Govoril jim je v oblačnem stebru; držali so se njegovih pričevanj in odredbe, ki jim jo je dal.
8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
Ti jim odgovarjaš, oh Gospod, naš Bog. Bil si jim Bog, ki odpušča, čeprav se maščuješ njihovim domiselnostim.
9 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.
Povišujte Gospoda, našega Boga in obožujte ga pri njegovi sveti gori, kajti Gospod, naš Bog, je svet.