< Zabura 99 >

1 Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
INkosi iyabusa; abantu kabathuthumele; ihlezi phakathi kwamakherubhi; umhlaba kawuzamazame.
2 Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
INkosi yinkulu eZiyoni; njalo iphakeme phezu kwezizwe zonke.
3 Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
Kazidumise ibizo lakho elikhulu lelesabekayo; lingcwele lona.
4 Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
Lamandla eNkosi athanda isahlulelo; wena umisa ukuqonda; wena wenza isahlulelo lokulunga kuJakobe.
5 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
Phakamisani iNkosi uNkulunkulu wethu, likhonze esenabelweni sezinyawo zayo. Ingcwele yona.
6 Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
UMozisi loAroni phakathi kwabapristi bayo, loSamuweli phakathi kwababiza ibizo layo, babiza iNkosi, yona yasibaphendula.
7 Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
Yakhuluma labo iphakathi kwensika yeyezi; bagcina izifakazelo zayo lesimiso eyabanika sona.
8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
Nkosi Nkulunkulu wethu, wena wabaphendula; waba nguNkulunkulu obathethelelayo, lanxa uphindisela ezenzweni zabo.
9 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.
Phakamisani iNkosi uNkulunkulu wethu, likhonze entabeni yayo engcwele; ngoba iNkosi uNkulunkulu wethu ingcwele.

< Zabura 99 >