< Zabura 99 >

1 Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
L’Éternel règne: les peuples tremblent; Il est assis sur les chérubins: la terre chancelle.
2 Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
L’Éternel est grand dans Sion, Il est élevé au-dessus de tous les peuples.
3 Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
Qu’on célèbre ton nom grand et redoutable! Il est saint!
4 Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
Qu’on célèbre la force du roi qui aime la justice! Tu affermis la droiture, Tu exerces en Jacob la justice et l’équité.
5 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
Exaltez l’Éternel, notre Dieu, Et prosternez-vous devant son marchepied! Il est saint!
6 Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
Moïse et Aaron parmi ses sacrificateurs, Et Samuel parmi ceux qui invoquaient son nom, Invoquèrent l’Éternel, et il les exauça.
7 Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
Il leur parla dans la colonne de nuée; Ils observèrent ses commandements Et la loi qu’il leur donna.
8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
Éternel, notre Dieu, tu les exauças, Tu fus pour eux un Dieu qui pardonne, Mais tu les as punis de leurs fautes.
9 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.
Exaltez l’Éternel, notre Dieu, Et prosternez-vous sur sa montagne sainte! Car il est saint, l’Éternel, notre Dieu!

< Zabura 99 >