< Zabura 99 >

1 Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
L’Éternel règne: que les peuples tremblent! Il est assis entre les chérubins: que la terre s’émeuve!
2 Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
L’Éternel est grand en Sion, et il est haut élevé par-dessus tous les peuples.
3 Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
Ils célébreront ton nom grand et terrible: – il est saint! –
4 Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
Et la force du roi qui aime la justice. Toi, tu établis la droiture, tu exerces le jugement et la justice en Jacob.
5 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
Exaltez l’Éternel, notre Dieu, et prosternez-vous devant le marchepied de ses pieds: – il est saint!
6 Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
Moïse et Aaron, parmi ses sacrificateurs, et Samuel, parmi ceux qui invoquent son nom, crièrent à l’Éternel, et il leur a répondu.
7 Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
Il leur parla dans la colonne de nuée: ils ont gardé ses témoignages, et le statut qu’il leur avait donné.
8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
Éternel, notre Dieu! tu leur as répondu, tu as été pour eux un Dieu qui pardonnait, et prenait vengeance de leurs actes.
9 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.
Exaltez l’Éternel, notre Dieu, et prosternez-vous en la montagne de sa sainteté; car l’Éternel, notre Dieu, est saint!

< Zabura 99 >