< Zabura 99 >
1 Ubangiji yana mulki, bari al’ummai su yi rawan jiki; yana zaune a kursiyi tsakanin kerubobi, bari duniya ta girgiza.
Jehovah hath reigned, peoples tremble, The Inhabitant of the cherubs, the earth shaketh.
2 Ubangiji mai girma yana a Sihiyona; an ɗaukaka shi a bisa dukan al’ummai.
Jehovah in Zion [is] great, And high He [is] over all the peoples.
3 Bari mu yabi girmanka da sunanka mai banrazana, shi mai tsarki ne.
They praise Thy name, 'Great, and fearful, holy [it] is.'
4 Sarki mai iko ne, yana ƙaunar adalci ka kafa gaskiya; a cikin Yaƙub ka yi abin da yake mai adalci da kuma daidai.
And the strength of the king Hath loved judgment, Thou — Thou hast established uprightness; Judgment and righteousness in Jacob, Thou — Thou hast done.
5 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi masa sujada a wurin sa ƙafafunsa; shi mai tsarki ne.
Exalt ye Jehovah our God, And bow yourselves at His footstool, holy [is] He.
6 Musa da Haruna suna cikin firistocinsa, Sama’ila yana cikin waɗanda suka kira bisa sunansa; sun kira ga Ubangiji ya kuwa amsa musu.
Moses and Aaron among His priests, And Samuel among those proclaiming His name. They are calling unto Jehovah, And He doth answer them.
7 Ya yi magana da su daga ginshiƙin girgije; ya kiyaye farillansa da ƙa’idodin da ya ba su.
In a pillar of cloud He speaketh unto them, They have kept His testimonies, And the statute He hath given to them.
8 Ya Ubangiji Allahnmu, ka amsa musu; ka kasance wa Isra’ila Allah mai gafartawa, ko da yake ka hukunta ayyukansu marasa kyau.
O Jehovah, our God, Thou hast afflicted them, A God forgiving Thou hast been to them, And taking vengeance on their actions.
9 Ku ɗaukaka Ubangiji Allahnmu ku kuma yi sujada a dutsensa mai tsarki, gama Ubangiji Allahnmu mai tsarki ne.
Exalt ye Jehovah our God, And bow yourselves at His holy hill, For holy [is] Jehovah our God!