< Zabura 98 >
1 Zabura ce. Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, gama ya yi abubuwa masu banmamaki; hannunsa na dama da hannunsa mai tsarki sun yi masa aikin ceto.
Cantád a Jehová canción nueva: porque ha hecho maravillas. Su diestra le ha salvado, y el brazo de su santidad.
2 Ubangiji ya sanar da cetonsa ya kuma bayyana adalcinsa ga al’ummai.
Jehová ha hecho notoria su salud: en ojos de las naciones ha descubierto su justicia.
3 Ya tuna da ƙaunarsa da kuma amincinsa ga gidan Isra’ila; dukan iyakar duniya sun ga ceton Allahnmu.
Háse acordado de su misericordia y de su verdad para con la casa de Israel: todos los términos de la tierra han visto la salud de nuestro Dios.
4 Ku yi sowa don farin ciki ga Ubangiji, dukan duniya, ku ɓarke da waƙa ta murna tare da kiɗi;
Cantád alegres a Jehová toda la tierra; gritád, y cantád, y decíd salmos.
5 ku yi kiɗi ga Ubangiji da garaya, da garaya da ƙarar rerawa,
Decíd salmos a Jehová con arpa: con arpa y voz de salmodia.
6 tare da bushe-bushe da karar ƙahon rago, ku yi sowa don farin ciki a gaban Ubangiji, Sarki.
Con trompetas, y sonido de bocina: cantád alegres delante del Rey Jehová.
7 Bari teku su yi ruri, da kuma kome da yake cikinsa, duniya da kuma kome da yake cikinta.
Brame la mar y su plenitud: el mundo y los que habitan en él.
8 Bari koguna su tafa hannuwansu, bari duwatsu su rera tare don farin ciki;
Los ríos batan las manos: juntamente hagan regocijo los montes,
9 bari su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa domin yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya da adalci mutane kuma cikin gaskiya.
Delante de Jehová; porque vino a juzgar la tierra: juzgará al mundo con justicia: y a los pueblos con rectitud.