< Zabura 98 >
1 Zabura ce. Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, gama ya yi abubuwa masu banmamaki; hannunsa na dama da hannunsa mai tsarki sun yi masa aikin ceto.
Salmo: Cantai ao SENHOR uma canção nova, porque ele fez maravilhas; sua mão direita e seu santo braço lhe fez ter a salvação.
2 Ubangiji ya sanar da cetonsa ya kuma bayyana adalcinsa ga al’ummai.
O SENHOR fez ser conhecida sua salvação; perante os olhos das nações ele mostrou sua justiça.
3 Ya tuna da ƙaunarsa da kuma amincinsa ga gidan Isra’ila; dukan iyakar duniya sun ga ceton Allahnmu.
Ele se lembrou de sua bondade e de sua fidelidade para com a casa de Israel; todos os confins da terra viram a salvação de nosso Deus.
4 Ku yi sowa don farin ciki ga Ubangiji, dukan duniya, ku ɓarke da waƙa ta murna tare da kiɗi;
Gritai de alegria ao SENHOR, toda a terra; clamai, cantai alegres, e tocai salmos.
5 ku yi kiɗi ga Ubangiji da garaya, da garaya da ƙarar rerawa,
Tocai ao SENHOR com harpa; com harpa, e com a voz da música;
6 tare da bushe-bushe da karar ƙahon rago, ku yi sowa don farin ciki a gaban Ubangiji, Sarki.
Com trombetas, e som de cornetas, clamai alegremente diante do Rei SENHOR.
7 Bari teku su yi ruri, da kuma kome da yake cikinsa, duniya da kuma kome da yake cikinta.
Faça barulho o mar com sua plenitude; o mundo com os que nele habitam.
8 Bari koguna su tafa hannuwansu, bari duwatsu su rera tare don farin ciki;
Que os rios batam palmas, que as montanhas juntamente se alegrem,
9 bari su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa domin yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya da adalci mutane kuma cikin gaskiya.
Diante do SENHOR, porque ele vem para julgar a terra; ele julgará ao mundo com justiça, e aos povos de forma correta.