< Zabura 98 >

1 Zabura ce. Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, gama ya yi abubuwa masu banmamaki; hannunsa na dama da hannunsa mai tsarki sun yi masa aikin ceto.
Nzembo. Boyembela Yawe nzembo ya sika, pamba te asalaka makambo ya kokamwa! Na nguya mpe na bokonzi na Ye ya bonzambe, alongaki.
2 Ubangiji ya sanar da cetonsa ya kuma bayyana adalcinsa ga al’ummai.
Yawe atalisaki elonga na Ye, amonisaki bosembo na Ye epai ya bikolo.
3 Ya tuna da ƙaunarsa da kuma amincinsa ga gidan Isra’ila; dukan iyakar duniya sun ga ceton Allahnmu.
Akanisaki bolingo mpe bosembo na Ye mpo na libota ya Isalaele. Kino na suka ya mokili, elonga ya Nzambe na biso emonanaki.
4 Ku yi sowa don farin ciki ga Ubangiji, dukan duniya, ku ɓarke da waƙa ta murna tare da kiɗi;
Mokili mobimba, bobetela Yawe maboko, boyemba banzembo ya esengo mpe bobeta mindule!
5 ku yi kiɗi ga Ubangiji da garaya, da garaya da ƙarar rerawa,
Bobetela Yawe lindanda, boyembela Ye banzembo na lokito ya nzenze!
6 tare da bushe-bushe da karar ƙahon rago, ku yi sowa don farin ciki a gaban Ubangiji, Sarki.
Bobeta maboko liboso ya Yawe, Mokonzi, na lokito ya bakelelo mpe ya maseke.
7 Bari teku su yi ruri, da kuma kome da yake cikinsa, duniya da kuma kome da yake cikinta.
Tika ete ebale monene elongo na nyonso oyo ezali kati na yango, mokili mpe bavandi na yango, bapesa lokito!
8 Bari koguna su tafa hannuwansu, bari duwatsu su rera tare don farin ciki;
Tika ete bibale ebeta maboko mpe bangomba nyonso eganga na esengo
9 bari su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa domin yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya da adalci mutane kuma cikin gaskiya.
liboso ya Yawe, pamba te azali koya kosambisa mabele! Akokata makambo na yango na bosembo.

< Zabura 98 >