< Zabura 98 >

1 Zabura ce. Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, gama ya yi abubuwa masu banmamaki; hannunsa na dama da hannunsa mai tsarki sun yi masa aikin ceto.
Ein Psalm. Singet Jehovah ein neues Lied; denn Wunder hat Er getan; gerettet hat Ihn Seine Rechte und der Arm Seiner Heiligkeit.
2 Ubangiji ya sanar da cetonsa ya kuma bayyana adalcinsa ga al’ummai.
Jehovah hat kundgetan Sein Heil; vor der Völkerschaften Augen hat Seine Gerechtigkeit Er geoffenbart.
3 Ya tuna da ƙaunarsa da kuma amincinsa ga gidan Isra’ila; dukan iyakar duniya sun ga ceton Allahnmu.
Er gedachte Seiner Barmherzigkeit und Seiner Wahrheit dem Hause Israels, alle Enden der Erde haben das Heil unseres Gottes gesehen.
4 Ku yi sowa don farin ciki ga Ubangiji, dukan duniya, ku ɓarke da waƙa ta murna tare da kiɗi;
Jubelt Jehovah, alle die Erde, brechet aus und lobpreiset und singet Psalmen!
5 ku yi kiɗi ga Ubangiji da garaya, da garaya da ƙarar rerawa,
Singt Psalmen dem Jehovah zur Harfe, auf der Harfe und des Psalmen Stimme.
6 tare da bushe-bushe da karar ƙahon rago, ku yi sowa don farin ciki a gaban Ubangiji, Sarki.
Mit Trompeten und Schall der Posaune jauchzet auf vor dem König Jehovah!
7 Bari teku su yi ruri, da kuma kome da yake cikinsa, duniya da kuma kome da yake cikinta.
Es brause Ihm das Meer und seine Fülle; die Welt und die darin wohnen.
8 Bari koguna su tafa hannuwansu, bari duwatsu su rera tare don farin ciki;
Die Flüsse sollen in die Hände klatschen, die Berge aufjubeln allzumal.
9 bari su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa domin yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya da adalci mutane kuma cikin gaskiya.
Vor Jehovah; denn Er kommt zu richten die Erde; Er richtet die Welt in Gerechtigkeit und die Völker in Geradheit.

< Zabura 98 >