< Zabura 98 >

1 Zabura ce. Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji, gama ya yi abubuwa masu banmamaki; hannunsa na dama da hannunsa mai tsarki sun yi masa aikin ceto.
Psaume à David (de David) lui-même.
2 Ubangiji ya sanar da cetonsa ya kuma bayyana adalcinsa ga al’ummai.
Le Seigneur a fait connaître son salut: en présence des nations, il a révélé sa justice.
3 Ya tuna da ƙaunarsa da kuma amincinsa ga gidan Isra’ila; dukan iyakar duniya sun ga ceton Allahnmu.
Il s’est souvenu de sa miséricorde et de sa vérité en faveur de la maison d’Israël.
4 Ku yi sowa don farin ciki ga Ubangiji, dukan duniya, ku ɓarke da waƙa ta murna tare da kiɗi;
Poussez des cris de joie vers Dieu, ô terre toute entière, chantez, et exultez, et jouez du psaltérion.
5 ku yi kiɗi ga Ubangiji da garaya, da garaya da ƙarar rerawa,
Chantez le Seigneur sur une harpe; sur une harpe, en y mêlant un chant de psaume;
6 tare da bushe-bushe da karar ƙahon rago, ku yi sowa don farin ciki a gaban Ubangiji, Sarki.
Sur des trompettes battues au marteau, et au son d’une trompette de corne.
7 Bari teku su yi ruri, da kuma kome da yake cikinsa, duniya da kuma kome da yake cikinta.
Que la mer soit agitée et sa plénitude, de même que le globe des terres et ceux qui y habitent.
8 Bari koguna su tafa hannuwansu, bari duwatsu su rera tare don farin ciki;
Les fleuves applaudiront de la main, comme aussi les montagnes exulteront
9 bari su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa domin yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya da adalci mutane kuma cikin gaskiya.
À la présence du Seigneur, parce qu’il vient juger la terre.

< Zabura 98 >