< Zabura 97 >
1 Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
RAB egemenlik sürüyor, coşsun yeryüzü, Bütün kıyı halkları sevinsin!
2 Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
Bulut ve zifiri karanlık sarmış çevresini, Doğruluk ve adalettir tahtının temeli.
3 Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
Ateş yürüyor O'nun önünde, Düşmanlarını yakıyor çevrede.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
Şimşekleri dünyayı aydınlatır, Yeryüzü görüp titrer.
5 Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
Dağlar balmumu gibi erir, RAB'bin, bütün yeryüzünün Rab'bi önünde.
6 Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
Gökler O'nun doğruluğunu duyurur, Bütün halklar görkemini görür.
7 Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
Utansın puta tapanlar, Değersiz putlarla övünenler! RAB'be tapın, ey bütün ilahlar!
8 Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
Siyon seviniyor yargılarını duyunca, ya RAB, Yahuda kentleri coşuyor.
9 Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
Çünkü sensin, ya RAB, bütün yeryüzünün en yücesi, Bütün ilahların üstündesin, çok ulusun.
10 Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Ey sizler, RAB'bi sevenler, kötülükten tiksinin. O sadık kullarının canını korur, Onları kötülerin elinden kurtarır.
11 An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
Doğrulara ışık, Temiz yüreklilere sevinç saçar.
12 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.
Ey doğrular, RAB'de sevinç bulun, Kutsallığını anarak O'na şükredin!