< Zabura 97 >

1 Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
Herren är Konung, dess fröjde sig jorden, och öarna fröjde sig, så månge som de äro.
2 Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
Moln och mörker är omkring honom; rättfärdighet och dom är hans stols stadfästelse.
3 Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
Eld går framför honom, och uppbränner hans ovänner allt omkring.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
Hans ljungande lyser på jordenes krets; jorden ser det, och förskräckes.
5 Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
Bergen försmälta såsom vax för Herranom; för hela jorderikes Herra.
6 Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
Himlarna förkunna hans rättfärdighet; och all folk se hans äro.
7 Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
Skämme sig alle de som belätom tjena, och berömma sig af afgudar; tillbedjer honom alle gudar.
8 Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
Zion hörer det, och är glad; och Juda döttrar fröjda sig, Herre, öfver ditt regemente.
9 Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
Ty du, Herre, äst den Högste i all land; du är fast upphöjd öfver alla gudar.
10 Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
I som älsken Herran, hater det onda; ( Herren ) bevarar sina heligas själar; ifrå de ogudaktigas hand skall han frälsa dem.
11 An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
Dem rättfärdiga skall alltid ljus uppgå igen, och frommom hjertom glädje.
12 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.
I rättfärdige, fröjder eder af Herranom, och tacker honom, och priser hans helighet.

< Zabura 97 >