< Zabura 97 >
1 Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
Yahwe anatawala; nchi ishangilie; visiwa vingi na vifurahi.
2 Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
Mawingu na giza vyamzunguka. Haki na hukumu ndio msingi wa kiti chake.
3 Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
Moto huenda mbele zake nao huwateketeza adui zake pande zote.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
Taa yake huangaza ulimwengu; nchi huona na kutetemeka.
5 Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
Milima huyeyuka kama nta mbele za Yahwe, Bwana wa dunia yote.
6 Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
Mbingu hutangaza haki yake, na mataifa yote huuona utukufu wake.
7 Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
Wale wote waabuduo sanamu za kuchonga wataaibishwa, wale wanao jivuna katika sanamu zisizo na maana mpigieni yeye magoti, enyi miungu wote!
8 Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
Sayuni ilisikia na kufurahi, na miji ya Yuda ilishangilia kwa sababu ya amri zako za haki, Yahwe.
9 Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
Kwa kuwa wewe, Yahwe, ndiye uliye juu sana, juu ya nchi yote. Umetukuka sana juu ya miungu yote.
10 Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Ninyi ambao mnampenda Yahwe, chukieni uovu! Yeye hulinda uhai wa watakatifu wake, naye huwatoa mikononi mwa waovu.
11 An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
Nuru imepandwa kwa ajili ya wenye haki na furaha kwa ajili ya wanyoofu wa moyo.
12 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.
Furahini katika Yahwe, enyi wenye haki; na mpeni shukurani mkumbukapo utakatifu wake.