< Zabura 97 >

1 Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
Il Signore regna, esulti la terra, gioiscano le isole tutte.
2 Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
Nubi e tenebre lo avvolgono, giustizia e diritto sono la base del suo trono.
3 Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
Davanti a lui cammina il fuoco e brucia tutt'intorno i suoi nemici.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
Le sue folgori rischiarano il mondo: vede e sussulta la terra.
5 Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
I monti fondono come cera davanti al Signore, davanti al Signore di tutta la terra.
6 Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
I cieli annunziano la sua giustizia e tutti i popoli contemplano la sua gloria.
7 Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
Siano confusi tutti gli adoratori di statue e chi si gloria dei propri idoli. Si prostrino a lui tutti gli dei!
8 Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
Ascolta Sion e ne gioisce, esultano le città di Giuda per i tuoi giudizi, Signore.
9 Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
Perché tu sei, Signore, l'Altissimo su tutta la terra, tu sei eccelso sopra tutti gli dei.
10 Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Odiate il male, voi che amate il Signore: lui che custodisce la vita dei suoi fedeli li strapperà dalle mani degli empi.
11 An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
Una luce si è levata per il giusto, gioia per i retti di cuore.
12 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.
Rallegratevi, giusti, nel Signore, rendete grazie al suo santo nome.

< Zabura 97 >