< Zabura 97 >

1 Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
TUHAN adalah Raja! Hendaklah bumi bergembira, dan pulau-pulau bersukacita.
2 Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
Ia dikelilingi awan dan kegelapan; keadilan dan hukum adalah azas pemerintahan-Nya.
3 Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
Api menjalar di hadapan-Nya, menghanguskan musuh di sekeliling-Nya.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
Kilatnya menerangi dunia, bumi gemetar melihat-Nya.
5 Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
Gunung-gunung meleleh seperti lilin di hadapan TUHAN, di hadapan TUHAN, penguasa seluruh bumi.
6 Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
Langit mewartakan keadilan-Nya, dan semua bangsa melihat kemuliaan-Nya.
7 Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
Semua orang yang menyembah berhala akan dipermalukan, yang membanggakan barang-barang yang tidak berguna; semua dewa akan sujud di hadapan TUHAN.
8 Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
Penduduk Sion dan kota-kota Yehuda senang ketika mendengar keputusan TUHAN.
9 Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
Sebab Engkau, ya TUHAN, penguasa seluruh bumi; Engkau agung melebihi segala dewa.
10 Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Hai kamu yang mencintai TUHAN, bencilah kejahatan! Sebab TUHAN melindungi hidup umat-Nya, Ia membebaskan mereka dari kuasa orang durhaka.
11 An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
Terang sudah terbit bagi orang yang tulus hati, dan sukacita untuk orang yang jujur.
12 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.
Bergembiralah, hai orang-orang yang tulus hati karena apa yang telah dilakukan TUHAN, dan bersyukurlah kepada Allah yang suci.

< Zabura 97 >