< Zabura 97 >
1 Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
Yahweh is the king! I want [everyone on] the earth to be glad/happy, and the [people who live on] the islands in the oceans to [also] rejoice [about that!]
2 Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
There are very dark clouds around him [to hide him]; he rules [MTY] righteously/justly and fairly.
3 Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
He [sends] fire in front of him, and he completely burns all his enemies in that fire.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
All around the world he causes lightning to flash; [people on] the earth see it, and it causes them to [be afraid and] tremble.
5 Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
The mountains/hills melt like wax in front of Yahweh, the one who is the Lord, [who rules] over all the earth.
6 Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
The [angels in] [MTY] heaven proclaim that he acts righteously, and all the people-groups see his glory.
7 Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
Everyone who worships idols should be ashamed; all those who are proud of their false gods [should realize that their gods are useless], [It is as though] all those gods bow down [to worship] Yahweh.
8 Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
[The people] [MTY] of Jerusalem hear [about Yahweh] and are glad/happy, and [people in the other] [MTY] cities in Judah [also] rejoice, because Yahweh judges [and punishes wicked people].
9 Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
Yahweh is the supreme [king] over all the earth; he has very great power, and all the [other] gods have no power at all.
10 Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Yahweh loves those who hate what [people do that] is evil; he protects the lives of his people, and he rescues them when the wicked [people try to harm them].
11 An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
His light shines on righteous [people]; he causes those who are righteous to rejoice.
12 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.
You righteous [people], rejoice about what Yahweh [has done], and thank him, our holy God!