< Zabura 97 >

1 Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
The LORD reigneth; let the earth rejoice; let the multitude of isles be glad.
2 Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
Clouds and darkness are round about him: righteousness and judgment are the foundation of his throne.
3 Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
A fire goeth before him, and burneth up his adversaries round about.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
His lightnings lightened the world: the earth saw, and trembled.
5 Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
The hills melted like wax at the presence of the LORD, at the presence of the Lord of the whole earth;
6 Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
The heavens declare his righteousness, and all the peoples have seen his glory.
7 Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
Ashamed be all they that serve graven images, that boast themselves of idols: worship him, all ye gods.
8 Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
Zion heard and was glad, and the daughters of Judah rejoiced; because of thy judgments, O LORD.
9 Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
For thou, LORD, art most high above all the earth: thou art exalted far above all gods.
10 Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
O ye that love the LORD, hate evil: he preserveth the souls of his saints; he delivereth them out of the hand of the wicked.
11 An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
Light is sown for the righteous, and gladness for the upright in heart.
12 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.
Be glad in the LORD, ye righteous; and give thanks to his holy name.

< Zabura 97 >