< Zabura 97 >

1 Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
For the same David, when his land was restored again to him. The Lord hath reigned, let the earth rejoice: let many islands be glad.
2 Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
Clouds and darkness are round about him: justice and judgment are the establishment of his throne.
3 Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
A fire shall go before him, and shall burn his enemies round about.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
His lightnings have shone forth to the world: the earth saw and trembled.
5 Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
The mountains melted like wax, at the presence of the Lord: at the presence of the Lord of all the earth.
6 Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
The heavens declared his justice: and all people saw his glory.
7 Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
Let them be all confounded that adore graven things, and that glory in their idols. Adore him, all you his angels:
8 Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
Sion heard, and was glad. And the daughters of Juda rejoiced, because of thy judgments, O Lord.
9 Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
For thou art the most high Lord over all the earth: thou art exalted exceedingly above all gods.
10 Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
You that love the Lord, hate evil: the Lord preserveth the souls of his saints, he will deliver them out of the hand of the sinner.
11 An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
Light is risen to the just, and joy to the right of heart.
12 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.
Rejoice, ye just, in the Lord: and give praise to the remembrance of his holiness.

< Zabura 97 >