< Zabura 97 >
1 Ubangiji yana mulki, bari duniya tă yi murna; bari tsibirai masu nesa su yi farin ciki.
The LORD reigns, let the earth rejoice; let the distant shores be glad.
2 Gizagizai da baƙin duhu sun kewaye shi; adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinsa.
Clouds and darkness surround Him; righteousness and justice are His throne’s foundation.
3 Wuta tana tafiya a gabansa tana kuma cinye maƙiyansa a kowane gefe.
Fire goes before Him and consumes His foes on every side.
4 Walƙiyarsa ta haskaka duniya; duniya ta gani ta kuma yi rawar jiki.
His lightning illuminates the world; the earth sees and trembles.
5 Duwatsu sun narke kamar kakin zuma a gaban Ubangiji, a gaban Ubangijin dukan duniya.
The mountains melt like wax at the presence of the LORD, before the Lord of all the earth.
6 Sammai sun yi shelar adalcinsa, dukan mutane kuma suka ga ɗaukakarsa.
The heavens proclaim His righteousness; all the peoples see His glory.
7 Dukan waɗanda suke bauta wa siffofi sun sha kunya, waɗanda suke fariya da gumaka, ku yi masa sujada, dukanku alloli!
All worshipers of images are put to shame— those who boast in idols. Worship Him, all you gods!
8 Sihiyona ta ji ta kuma yi farin ciki kuma dukan ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukunce-hukuncenka, ya Ubangiji.
Zion hears and rejoices, and the towns of Judah exult because of Your judgments, O LORD.
9 Gama kai, ya Ubangiji, kai ne Mafi Ɗaukaka a bisa dukan duniya; ana darjanta ka fiye da dukan alloli.
For You, O LORD, are Most High over all the earth; You are exalted far above all gods.
10 Bari masu ƙaunar Ubangiji su ƙi mugunta, gama yana tsaron rayukan amintattunsa yana kuma kuɓutar da su daga hannun mugaye.
Hate evil, O you who love the LORD! He preserves the souls of His saints; He delivers them from the hand of the wicked.
11 An haskaka haske a kan masu adalci da kuma farin ciki a kan masu gaskiya a zuciya.
Light shines on the righteous, gladness on the upright in heart.
12 Ku yi farin ciki a cikin Ubangiji, ku da kuke masu adalci, ku kuma yabi sunansa mai tsarki.
Rejoice in the LORD, you righteous ones, and praise His holy name.