< Zabura 96 >

1 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
Cantád a Jehová canción nueva: cantád a Jehová toda la tierra.
2 Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Cantád a Jehová, bendecíd su nombre: anunciád de día en día su salud.
3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
Contád en las naciones su gloria: en todos los pueblos sus maravillas.
4 Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Porque grande es Jehová, y muy alabado: terrible sobre todos los dioses.
5 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
Porque todos los dioses de los pueblos son ídolos: mas Jehová hizo los cielos.
6 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
Alabanza y gloria está delante de él: fortaleza y gloria está en su santuario.
7 Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
Dad a Jehová, o! familias de los pueblos, dad a Jehová la gloria y la fortaleza.
8 Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
Dad a Jehová la honra de su nombre: tomád presentes, y veníd a sus patios.
9 Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
Encorváos a Jehová en la hermosura de su santuario: teméd delante de él toda la tierra.
10 Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
Decíd en las naciones: Jehová reinó, también compuso el mundo, no se meneará: juzgará a los pueblos en justicia.
11 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
Alégrense los cielos, y regocíjese la tierra: brame la mar y su plenitud.
12 bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
Regocíjese el campo y todo lo que en él está: entonces exultarán todos los árboles de la breña,
13 za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.
Delante de Jehová que vino: porque vino a juzgar la tierra. Juzgará al mundo con justicia, y a los pueblos con su verdad.

< Zabura 96 >