< Zabura 96 >

1 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
¡Canten a Yavé un canto nuevo! ¡Cante a Yavé toda la tierra!
2 Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
¡Canten a Yavé, bendigan su Nombre! Anuncien de día en día su salvación.
3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
Proclamen su gloria entre las naciones, Entre todos los pueblos, sus maravillosas obras.
4 Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Porque grande es Yavé Y digno de suprema alabanza. Él debe ser temido por encima de todos los ʼelohim.
5 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
Porque todos los ʼelohim de los pueblos son ídolos. Pero Yavé hizo los cielos.
6 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
Esplendor y majestad hay ante Él. Fortaleza y hermosura hay en su Santuario.
7 Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
Tributen a Yavé, oh familias de los pueblos. Tributen a Yavé gloria y fortaleza.
8 Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
Tributen a Yavé la gloria debida a su Nombre. Lleven ofrenda y entren en sus patios.
9 Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
Adoren a Yavé en la hermosura de la santidad. Tiemble ante Él toda la tierra.
10 Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
Digan entre las naciones: ¡Yavé reina! Ciertamente el mundo está firmemente establecido. No será conmovido. Él juzgará a los pueblos con equidad.
11 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
¡Alégrense los cielos Y regocíjese la tierra! Brame el mar y todo lo que contiene.
12 bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
Exáltese el campo y todo lo que hay en él. Entonces todos los árboles del bosque cantarán con gozo
13 za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.
Delante de Yavé Quien viene, Porque viene a juzgar la tierra. Él juzgará al mundo con justicia Y a los pueblos con su fidelidad.

< Zabura 96 >