< Zabura 96 >

1 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
Cantai ao Senhor um cântico novo, cantai ao Senhor toda a terra.
2 Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Cantai ao Senhor, bendizei o seu nome; anunciai a sua salvação de dia em dia.
3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
Anunciai entre as nações a sua glória; entre todos os povos as suas maravilhas.
4 Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Porque grande é o Senhor, e digno de louvor, mais tremendo do que todos os deuses.
5 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
Porque todos os deuses dos povos são ídolos, mas o Senhor fez os céus.
6 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
Glória e magestade estão ante a sua face, força e formosura no seu santuário.
7 Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
Dai ao Senhor, ó famílias dos povos, dai ao Senhor glória e força.
8 Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
Dai ao Senhor a glória devida ao seu nome: trazei oferenda, e entrai nos seus átrios.
9 Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
Adorai ao Senhor na beleza da santidade: tremei diante dele toda a terra.
10 Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
Dizei entre as nações que o Senhor reina: o mundo também se firmará para que se não abale: julgará os povos com retidão.
11 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
Alegrem-se os céus, e regozije-se a terra: brama o mar e a sua plenitude.
12 bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
Alegre-se o campo com tudo o que há nele: então se regozijarão todas as árvores do bosque,
13 za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.
Ante a face do Senhor, porque vem, porque vem a julgar a terra: julgará o mundo com justiça e os povos com a sua verdade.

< Zabura 96 >