< Zabura 96 >

1 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
Singet dem HERRN ein neues Lied, singet dem HERRN, alle Lande!
2 Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Singt dem HERRN, preist seinen Namen, verkündet Tag für Tag sein Heil!
3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
Erzählt von seiner Herrlichkeit unter den Heiden, unter allen Völkern seine Wundertaten!
4 Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Denn groß ist der HERR und hoch zu preisen, mehr zu fürchten als alle andern Götter;
5 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
denn alle Götter der Heiden sind nichtige Götzen, doch der HERR hat den Himmel geschaffen.
6 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
Hoheit und Pracht gehn vor ihm her, Macht und Herrlichkeit füllen sein Heiligtum.
7 Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
Bringt dar dem HERRN, ihr Geschlechter der Völker, bringt dar dem HERRN Ehre und Preis!
8 Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
Bringt dar dem HERRN die Ehre seines Namens, bringt Opfergaben und kommt in seine Vorhöfe!
9 Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
Werft vor dem HERRN euch nieder in heiligem Schmuck, erzittert vor ihm, alle Lande!
10 Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
Verkündet unter den Heiden: »Der HERR ist König! Und feststehn wird der Erdkreis, daß er nicht wankt; richten wird er die Völker nach Gebühr.«
11 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
Des freue sich der Himmel, die Erde jauchze, es brause das Meer und was darin wimmelt!
12 bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
Es jauchze die Flur und was auf ihr wächst! Dann werden auch jubeln alle Bäume des Waldes
13 za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.
vor dem HERRN, wenn er kommt, wenn er kommt, zu richten die Erde. Richten wird er den Erdkreis mit Gerechtigkeit und die Völker mit seiner Treue.

< Zabura 96 >