< Zabura 96 >
1 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
Chantez à l’Éternel un cantique nouveau; chantez à l’Éternel, toute la terre!
2 Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Chantez à l’Éternel, bénissez son nom, annoncez de jour en jour son salut!
3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
Racontez parmi les nations sa gloire, parmi tous les peuples ses œuvres merveilleuses.
4 Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
Car l’Éternel est grand, et fort digne de louange; il est terrible par-dessus tous les dieux.
5 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
Car tous les dieux des peuples sont des idoles, mais l’Éternel a fait les cieux.
6 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
La majesté et la magnificence sont devant lui, la force et la beauté sont dans son sanctuaire.
7 Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
Familles des peuples, rendez à l’Éternel, rendez à l’Éternel la gloire et la force!
8 Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
Rendez à l’Éternel la gloire de son nom; apportez une offrande et entrez dans ses parvis.
9 Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
Adorez l’Éternel en sainte magnificence; tremblez devant lui, toute la terre.
10 Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
Dites parmi les nations: L’Éternel règne! Aussi le monde est affermi, il ne sera pas ébranlé. Il exercera le jugement sur les peuples avec droiture.
11 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
Que les cieux se réjouissent, et que la terre s’égaie; que la mer bruie, et tout ce qui la remplit;
12 bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
Que les champs se réjouissent, et tout ce qui est en eux! Alors tous les arbres de la forêt chanteront de joie,
13 za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.
Devant l’Éternel; car il vient, car il vient pour juger la terre: il jugera le monde avec justice, et les peuples selon sa fidélité.