< Zabura 96 >

1 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
Oh sing unto the Lord a new song: sing unto the Lord, all the lands.
2 Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Sing unto the Lord, bless his name: announce from day to day his salvation.
3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
Relate among the nations his honor, among all the people his wonders.
4 Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
For the Lord is great, and greatly praised: he is to be feared above all gods.
5 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
For all the gods of the nations are idols; but the Lord hath made the heavens.
6 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
Glory and majesty are before him: strength and beauty are in his sanctuary.
7 Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
Ascribe unto the Lord, O ye families of the people, ascribe unto the Lord honor and strength.
8 Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
Ascribe unto the Lord the honor [due unto] his name: bear hither a present, and come unto his courts.
9 Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
Bow down unto the Lord in the beauty of holiness: tremble before him, all ye lands.
10 Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
Say among the nations, “The Lord reigneth;” [therefore] also the world is ever firmly established that it shall hot be moved: he will judge the people in equity.
11 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
Let the heavens rejoice, and let the earth be glad: let the sea roar, with all that filleth it.
12 bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
Let the field exult, and all that is therein: then shall all the trees of the forest sing for joy,
13 za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.
Before the Lord; for he cometh, for he cometh to judge the earth: he will judge the world with righteousness, and people in his truth.

< Zabura 96 >