< Zabura 96 >
1 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
When the house was built after the Captivity, a Song of David. Sing to the Lord a new song; sing to the Lord, all the earth.
2 Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Sing to the Lord, bless his name: proclaim his salvation from day to day.
3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
Publish his glory among the Gentiles, his wonderful works among all people.
4 Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
For the Lord is great, and greatly to be praised: he is terrible above all gods.
5 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
For all the gods of the heathen are devils: but the Lord made the heavens.
6 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
Thanksgiving and beauty are before him: holiness and majesty are in his sanctuary.
7 Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
Bring to the Lord, you families of the Gentiles, bring to the Lord glory and honor.
8 Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
Bring to the Lord the glory [becoming] his name: take offerings, and go into his courts.
9 Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
Worship the Lord in his holy court: let all the earth tremble before him.
10 Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
Say among the heathen, The Lord reigns: for he has established the world so that it shall not be moved: he shall judge the people in righteousness.
11 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
Let the heavens rejoice, and the earth exult; let the sea be moved, and the fullness of it.
12 bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
The plains shall rejoice, and all things in them: then shall all the trees of the wood exult before the presence of the Lord:
13 za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.
for he comes, for he comes to judge the earth; he shall judge the world in righteousness, and the people with his truth.