< Zabura 96 >

1 Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
A canticle for David himself, when the house was built after the captivity. Sing ye to the Lord a new canticle: sing to the Lord, all the earth.
2 Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
Sing ye to the Lord and bless his name: shew forth his salvation from day to day.
3 Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
Declare his glory among the Gentiles: his wonders among all people.
4 Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
For the Lord is great, and exceedingly to be praised: he is to be feared above all gods.
5 Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
For all the gods of the Gentiles are devils: but the Lord made the heavens.
6 Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
Praise and beauty are before him: holiness and majesty in his sanctuary.
7 Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
Bring ye to the Lord, O ye kindreds of the Gentiles, bring ye to the Lord glory and honour:
8 Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
Bring to the Lord glory unto his name. Bring up sacrifices, and come into his courts:
9 Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
Adore ye the Lord in his holy court. Let all the earth be moved at his presence.
10 Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
Say ye among the Gentiles, the Lord hath reigned. For he hath corrected the world, which shall not be moved: he will judge the people with justice.
11 Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
Let the heavens rejoice, and let the earth be glad, let the sea be moved, and the fulness thereof:
12 bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
The fields and all things that are in them shall be joyful. Then shall all the trees of the woods rejoice
13 za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.
Before the face of the Lord, because he cometh: because he cometh to judge the earth. He shall judge the world with justice, and the people with his truth.

< Zabura 96 >